Aminiya:
2025-11-03@03:11:34 GMT

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci

Published: 6th, April 2025 GMT

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wasu ƙauyuka na Ƙaramar Hukumar Bokkos da ke Jihar Filato.

Ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Ruwi, Manguna, Daffo, Josho da Hurti.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba Fasinja ya yi ƙoƙarin buɗe ƙofar jirgi a sararin samaniya

Shugaban ƙungiyar kuma gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana waɗannan hare-hare a matsayin rashin hankali da tausayi.

Ya ce an kashe mutane da dama ciki har da mata da yara, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Ya ƙara da cewa irin waɗannan hare-hare na barazana ga zaman lafiya da haɗin kan yankin Arewa.

A wata sanarwa da kakakinsa, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a Gombe, Gwamna Yahaya ya bayyana jimaminsa game da wannan mummunan lamari.

Ya jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa da kuma gwamnatin Jihar Filato da al’ummarta baki ɗaya.

Gwamnan ya bayyana damuwarsa kan yadda rikici ke ci gaba da addabar yankunan karkara, musamman yadda ake yawan zubar da jinin bayin Allah.

“Rayuwar ɗan Adam abu ce girma da ba za a yi wasa da ita ba. Waɗannan mugayen hare-hare da ake kai wa mutane abin Allah-wadai ne, kuma dole ne a dakatar da su,” in ji Gwamna Yahaya.

Ya yaba da matakin gaggawa da Gwamna Caleb Mutfwang na Jihar Filato, ya ɗauka bayan faruwar lamarin, da kuma ƙoƙarin jami’an tsaro wajen shawo kan rikicin.

Sai dai ya buƙaci jami’an tsaro da su ƙara himma wajen kamo waɗanda suka aikata wannan aika-aika tare da tabbatar da cewa an hukunta su.

Gwamna Yahaya ya kuma buƙaci a ƙara ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan zaman lafiya, haƙuri da fahimtar juna a tsakanin al’umma, musamman tsakanin manoma da makiyaya.

Ya jaddada ƙudirin gwamnonin Arewa na aiki tare wajen kawo ƙarshen rikice-rikice, ta hanyar ƙarfafa tsaro, tattaunawa da aiwatar da manufofin da za su kawo zaman lafiya da haɗin kai.

Ya kuma buƙaci shugabannin al’umma, ƙungiyoyin addinai da na fararen hula da su tallafa wa gwamnati ta hanyar yaɗa sakon zaman lafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnonin Arewa hare hare Inuwa Yahaya zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Duk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa.

 

Wannan matsala ta daɗe tana jawo muhawara tsakanin iyaye, malamai da hukumomin ilimi.

Wasu na ganin matsaloli ne da ba za su rasa nasaba da rashin kulawa da watsi da harkar ilimi da gwamnati ta yi ba.

Ko wadanne dalilai ne suka daliban makarantun masu zaman kansu suka fi kokari idan aka kwatanta da daliban makarantu na gwamnati?

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa PDP Ta Ki Sayarwa Sule Lamido Fom Din Takarar Shugaban Jam’iyya

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari