Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Kananan Cibiyoyin Kiwon Lafiya 8,880 A Duka Fadin Kasar
Published: 6th, April 2025 GMT
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwan cewa ta ware kudade don gina kananan cibiyoyin kiwon lafiya a duk fadin kasar.
Jaridar daily Trust ta Najeriya ta nakalto mataimakin shugaban kasa Alhaji Shetima yana fadar haka a ranar Asabar a lokacinda yake kaddamar da cibiyar yaki da cutar daga a cikin asbitin koyon aikin likitanci ta OOUTH dage birnin shagamu na jihar Oyo.
Mataimakin shugaban kasar ya kara da cewa shirin gina wadannan kananan cibiyoyin kiwon lafiya dai yana daga cikin babban shirin gwamnatin mai ci na kyautata cibiyoyin kiwon lafiya a kasar gaba daya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kakkausan martanin da Iran ta mayar ya tabbatar da cewa babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani ba
Izzat al-Rishq mamba na ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya jaddada cewa: Kakkausan martanin da Iraniyawa suka mayar ya tabbatar da cewa; babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani kan zaluncinsa ba, kuma babu wuce gona da iri ba tare da hukunci ba.
Izzat al-Rishq ya yi nuni da cewa: Tabbas makamai masu linzami da jiragen saman yaki marasa matuka ciki na Iran sun yi nasarar kai wa cikin tsakiyar haramtacciyar kasar Isra’ila, duk kuwa da kace-nacen da ake yi na girke na’urorin kakkabo makamai a haramtacciyar kasar Isra’ila musamman Iron Dome, Arrow da David’s Sling.
Al-Rashq ya kuma bayyana cewa: Tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila ya gaza shawo kan hare-haren da Iran suka kai, kuma a halin yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila tana fama da gobarar da ta kunna a tsakanin al’ummomin yankin. A karshe ya jaddada cewa: Sakon a bayyane yake: Duk wanda ya yi tsokana, to tantana kudarsa.