“A yau ne Gwamna Dauda Lawal ya fara rangaɗin wuraren haƙar ma’adanai da masana’antu, inda ya fara ziyarar aiki a wani kamfani mai zaman kansa na Comet Star Industry da ke Ƙaramar Hukumar Anka.

 

“Ma’aikatar, mallakin Prince James Uduji OON, tana sarrafa kusan tan 1,000 a kullum. Tana da cikakkun kayan aiki da sabbin fasahohin haƙar ma’adinai don tabbatar da gudanar da ayyuka masu inganci.

“Lokacin da ya je masana’antar, Gwamna Lawal ya zagaya wurare da dama, inda ya fara tun daga magudanar ruwa da zuwa duka sassan injina da kayan aiki.

 

“Gwamna Lawal ya kuma ziyarci wurare daban-daban a cikin masana’antar, ciki har da gidan wutar lantarki da ke samar da wutar lantarki ga ɗaukacin kamfanin, da ɗakin gwaje-gwajen da ake sarrafa kayayyakin.”

 

A jawabinsa jim kaɗan bayan kammala rangaɗin, Gwamna Lawal ya bayyana gamsuwarsa da ƙa’idojin masana’antar, inda ya bayyana cewa irin jarin da gwamnatin jihar ke nema kenan.

 

“Na ji daɗi a yau domin wannan ya nuna ƙarara cewa an samu nasara a fannin tsaro a jihar Zamfara, ina godiya ga sojoji da duk masu ruwa da tsaki da suke aiki tuƙuru domin samar da zaman lafiya.

 

“Bugu da ƙari, ana ci gaba da tattaunawa tsakanin Gwamnatin Tarayya, Gwamnatin Jiha, kamfanoni masu zaman kansu, da sauran al’umma don fahimtar kadarorinmu da kuma gano alfanun su, wannan jiha tana da albarkar ma’adanai masu inganci, idan har za mu iya gano amfani su, ina tabbatar muku cewa za mu inganta kuɗaɗen shiga da kuma bunƙasa jihar Zamfara cikin sauri.”

 

A Ƙaramar Hukumar Maru, Gwamna Dauda Lawal ya yi wa masu haƙar ma’adan alƙawarin cikakken goyon bayan gwamnati, matuƙar suna aiki yadda doka da ƙayyade

 

Gwamnan ya yi alƙawarin samar wa da ma’aikatan muhimman kayan aiki don kauce wa gurɓatar muhalli.

Ya ce, “Muna haɗin gwiwa da gwamnatin yarayya, kuma suna ɗaukar muhimman matakai don aiwatar da abubuwan da suka wajaba. Zan turo Kwamishinan muhalli ya zauna da kuma, ta yadda kowa zai iya yin rajista. Ta hanyar rajista ne kawai za mu iya taskace sahihan bayanai.

 

“Gwamnatin jiha za ta samar maku da tallafin da ya wajaba, wanda zai haɗa da samo maku mataƙaicin izinin aikin haƙar ma’adanan daga gwamnatin tarayya, amma dole sai kun kafa ƙungiyoyin taimakon kai da kai.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Lawal

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.

Daga Abdullahi Shettima

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya wakilci Nijeriya a taron ƙoli na biranen Asiya da ya gudana a ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), inda ya gabatar da kudirorin sauyin ci gaban Kaduna.

Taron ya samu halartar manyan baki daga ƙasashe sama da 150, ciki har da gwamnoni, shugabannin birane da jagororin kasuwanci daga Asiya, Fasifik, Turai da Afirka. Taken taron shi ne “Haɗin Gwiwa. Ƙarfafawa. Sauyi.”

A jawabinsa mai taken “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa,” Gwamna Uba Sani ya bayyana yadda Kaduna ke samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma da tallafawa jama’a. Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki, kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su cim ma nasara a rayuwarsu.

Haka kuma, ya halarci baje kolin birnin Dubai mai taken “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira da Tasirin Zamantakewa,” inda ya jaddada muhimmancin jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha wajen buɗe damarmaki ga al’umma.

A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta-Janar na birnin Dubai, inda suka tattauna batutuwan kirkirar makamashin sharar gida, kula da sharar zamani, da tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.

Duk ɓangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin tattalin arzikin Kaduna zuwa mai ɗorewa.

Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun gaba wajen yin haɗin kai, ƙirƙira da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa — a Najeriya da duniya baki ɗaya.

Karshe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba