Ayatullah Khatami: Jerin Gwanon Ranar Qudus Rana Ce Mai Matukar Muhimmaci A Musulunci
Published: 29th, March 2025 GMT
Wanda ya jagoranci sallar juma’a a nan Tehran a jiya Juma’a ya bayyana cewa; Jerin gwanon ranar Kudus tana da matukar muhimmanci a addinin musulunci, yana mai kara da cewa: Muna godewa Allah madaukakin sarki cewa, ranar kudus ta wannan shekarar ta bunkasa fiye da shekarun baya.”
Haka nan kuma ya kara da cewa; Imam Khumaini ( r.
Limamin na Tehran ya kuma kara da cewa, abinda Imam Khumain ( r.a) ya yi na ayyana ranar Kudus, wata hikima ce wacce ta dakile makarkashiyar da makiya su ka kitsa.
Ayatullah Khatami ya kuma yi ishara da yadda aka yi jerin gwanon na ranar Kudus a cikin garuruwa da birane 900 a cikin fadin Iran.
A fadin duniya kuwa limamin na Tehran ya yi ishara da cewa an yi jerin gwanon ranar Kudus a cikin kasashe 80 da su ka hada Amurka, Birtaniya, Faransa da kuma Jamus.
Dangane da barazanar da shugaban kasar Amurka yake yi wa Iran, limamin na Tehran ya ce, babu abinda ya iya sai barazana saboda halinsa na tsoro, kuma abin mamaki ne a ce har yanzu bai san cewa, barazanarsa ba ta da wani tasiri ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ranar Kudus
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.
Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.
An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.
“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.
Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.
Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.
Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.
An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.
Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.