Wanda ya jagoranci sallar juma’a a nan Tehran a jiya Juma’a ya bayyana cewa; Jerin gwanon ranar Kudus tana da matukar muhimmanci a addinin musulunci, yana mai kara da cewa: Muna godewa Allah madaukakin sarki cewa, ranar kudus ta wannan shekarar ta bunkasa fiye da shekarun baya.”

Haka nan kuma ya kara da cewa; Imam Khumaini ( r.

a) da ya ayyana ranar Kudus a duniya a 1979, wacce ita ce juma’ar karshe ta watan Ramadan, a wancan lokacin manyan kasashen duniya masu takama da karfi suna kokarin ganin an mance da batun Falasdinu da kuma kasakantar da shi da cewa batu ne na Larabawa kadai.

Limamin na Tehran ya kuma kara da cewa, abinda Imam Khumain ( r.a) ya yi na ayyana ranar Kudus, wata hikima ce wacce ta dakile makarkashiyar da makiya su ka kitsa.

Ayatullah Khatami ya kuma yi ishara da yadda aka yi jerin gwanon na ranar Kudus a cikin garuruwa da birane 900 a cikin fadin Iran.

A fadin duniya kuwa limamin na Tehran ya yi ishara da cewa an yi jerin gwanon ranar Kudus a cikin kasashe 80 da su ka hada Amurka, Birtaniya, Faransa da kuma Jamus.

Dangane da barazanar da shugaban kasar Amurka yake yi wa Iran, limamin na Tehran ya ce, babu abinda ya iya sai barazana saboda halinsa na tsoro, kuma abin mamaki ne a ce har yanzu bai san cewa, barazanarsa  ba ta da wani tasiri ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ranar Kudus

এছাড়াও পড়ুন:

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wadannan ’yan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi sun sake nuna bajintar da kasar Sin ke nunawa a fagen kere-keren mutum-mutumi masu siffar dan’adam da kuma yadda masana’antar bangarensu ke samun ci gaba cikin hanzari a kasar.

A watan Agusta mai kamawa ne kasar Sin za ta karbi bakuncin gasar wasannin motsa jiki na mutum-mutumi masu siffar dan’adam. Kuma wannan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi da aka gwabza fafatawar karshe a dandalin wasannin motsa jiki na fasahar zamani da ke birnin Beijing, wata kyakkyawar shaida ce a kan yadda kasar ta shirya wa karbar bakuncin wannan gasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  •  Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus
  • Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa