HausaTv:
2025-05-01@01:17:38 GMT

Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas

Published: 27th, March 2025 GMT

Bayanai daga falasdinu na cewa an kashe Hamas Abdul-Latif al-Qanou wani kakakin kungiyar Hamas a wani harin da Isra’ila ta kai a arewacin Gaza.

Kamfanin dillancin labaran Quds na Falasdinu ya bayar da rahoton  cewa, jami’in ya yi shahada ne a wani harin da Isra’ila ta kai ta sama a kan tantinsa a garin Jabalia da ke arewacin zirin Gaza.

Har ila yau harin ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da suka hada da kananan yara.

Wannan kisan dai shi ne na baya bayan nan a jerin hare-haren wuce gona da irin da gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da yi a zirin Gaza tun a watan Oktoban shekarar 2023, bayan wani dan takaitaccen lokaci inda ta saba ka’idojin tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas, tare da kai munanan hare-hare.

Shahadar al-Qanou ta zo ne kwanaki kadan bayan kisan gillar da gwamnatin sahyoniyawan ta yi wa wasu fitattun jami’an ofishin siyasa na Hamas, wato Ismail Barhoum da Salah al-Bardaweel. An kashe su duka a samame daban-daban.

A baya-bayan nan dai babban mai magana da yawun kungiyar Hamas Sami Abu Zuhri ya jaddada cewa kisan gilla ba zai hana kungiyar ci gaba da fafutukar kwato yankunan Falasdinawa ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe masu zaman makoki bakwai tare da jikkata wasu a ƙauyen Kopl da ke Ƙaramar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.

Shugaban Karamar Hukumar, Honorabul Modu Mustapha, ya ce mayaƙan sun buɗe wa mutanen wuta ne a yammacin ranar Litinin, a yayin da suke shirin gudanar da addu’o’i ga ’yan uwansu da suka rasu.

Ya ce, “Sun taru ne domin yin addu’a lokacin da ’yan ta’addan suka sauka a kansu. Mun kwashe mutane da yawa da suka samu raunukan harsashi zuwa Babban Asibitin Mubi da ke maƙwabtaka da Jihar Adamawa.

“Adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, saboda wasu sun tsere cikin daji da raunukan harsashi. Ana ci gaba da aikin nemowa da ceto waɗanda ke cikin daji,” in ji shi.

Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu

Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ci gaba da yin Allah wadai da hare-haren, inda ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin da ya wuce tunanin dan Adam.

“Ko jiya ma, na samu kiran gaggawa cewa an kashe sama da ’yan banga 10 a wani yankin da ke tsakanin Karamar Hukumar Hawul ta Jihar Borno da garin Garkida a Jihar Adamawa.

“Al’ummata na fama da munanan asara ba tare da wani faɗa ba. A cikin wata guda da ya gabata kaɗai, an kashe sama da mutum dari a hare-hare da dama yankunan Sabon Gari da Izge da Kirawa da Pulka da Damboada Chibok da Askira Uba da wasu da yawa da ba zan iya lissafawa ba,” in ji Sanata Ndume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba