HausaTv:
2025-06-15@18:13:27 GMT

Ranar Quds : Hamas ta bukaci masu huduba su sadaukar da jawabansu kan Falastinu

Published: 27th, March 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi kira hadin kan kasashen duniya domin nuna goyon baya ga Falasdinu gabanin ranar Kudus ta Duniya.

Kungiyar ta yi kira da a samar da hadin kai a kasashen duniya a ranar Juma’a da Asabar da Lahadi masu zuwa domin nuna goyon baya ga Gaza da Kudus, yayin da Isra’ila tare da goyon bayan Amurka ke ci gaba da yakin kisan kare dangi da suke yi wa Falasdinawa.

A cikin sanarwar da ta fitar, Hamas ta yi kira da a gudanar da gagarumin jerin gwano na hadin gwiwa a dukkan birane da manyan birane na duniya.

“Muna kira ga daukacin al’ummar Falasdinu, kasashen Larabawa da na Musulunci, da dukkan al’ummarmu masu son ‘yanci na duniya da su fito a ranar Juma’a, Asabar, da Lahadi mai zuwa don kare Gaza, Quds, da masallacin Aqsa, da goyon bayan juriyar jama’armu, da yin tir da laifuffuka da tsare-tsare na gwamnatin mulkin mallaka a kan kasarmu, mutanenmu, da wurarenmu masu tsarki da ake yi a Gaza.” Inji Hamas

Hamas ta kuma yi kira da a ci gaba da matsin lamba ga gwamnatin Isra’ila don kawo karshen zalunci da kisan kiyashi ga Palasdinawa, Har ila yau sanarwar ta yi kira ga masu hudubar sallar Juma’a da su sadaukar da jawabansu na wannan Juma’a kan batun Falastinu, domin kwadaitar da al’ummar musulmi wajen karfafa goyon bayansu ga al’ummar Palastinu da suke fafutukar kare kasarsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya