Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
Published: 27th, March 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na tallafawa shirin inganta ilimi na bunkasa Afirka (BEAR) III, wani shiri na hadin gwiwa da hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) da Jamhuriyar Koriya suka yi.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan wayar da kan jama’a ma’aikatar ilimi ta jihar Kano Balarabe Abdullahi Kiru, yace aikin yana da nufin haɓaka ilimin fasaha da na sana’a a faɗin Afirka, tare da mai da hankali kan ƙarfafa tsarin ilimin fasaha da na sana’a da horo (TVET).
Aikin zai mayar da hankali ne kan harkar noma, tare da mai da hankali kan sarrafa kayan noma da sarrafa su bayan girbi.
A cewar Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda, shirin na BEAR III ya yi daidai da ajandar Gwamna Abba Kabir Yusuf na inganta shirye-shiryen koyon sana’o’i don dogaro da kai.
Ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kano za ta ci gaba da hada gwiwa da hukumar UNESCO da kasar Koriya ta Kudu domin bunkasa koyar da sana’o’i a makarantun furamare da na gaba da sakandare a fadin jihar.
Darakta a ma’aikatar ilimi ta tarayya Dr. (Mrs) M.A Olodo ta jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano domin gudanar da taro da masu ruwa da tsaki dangane da aiwatar da shirin na BEAR III.
Ta ba da tabbacin cewa ƙungiyar za ta yi amfani da mafi kyawun lokacin da ya rage don cimma manufofin aikin.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, an gina aikin na BEAR III akan ginshikai guda uku: sanya aikin ya dace da bukatun kasashe masu cin gajiyar shirin, da inganta TVET da ake bayarwa, da kuma kyautata fahimtarsa a tsakanin matasa.
Za a gudanar da aikin a kasashe hudu na yammacin Afirka: Najeriya, Ghana, Cote d’Ivoire, da Saliyo.
Rel/ Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya sheƙar da ’yan siyasa daga ɓangarori daban-daban suke yi.
A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa Jam’iyyar APC mai mulki ta jawo ɗiga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaɓen 2027.
Hakan dai yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu ’yan ƙasar suke kokawa bisa yadda ake gudanar da mulki da kuma yadda wasu manyan ’yan siyasa suke fadi-tashin kafa wata inuwa da suka ce za ta ciro wa talaka kitse a wuta ta hanyar kawar da gwamnatin APC.
NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaWannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai da nufin gano alƙiblar da siyasar Najeriya take shirin fuskanta.
Domin sauke shirin. Latsa nan