Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
Published: 27th, March 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na tallafawa shirin inganta ilimi na bunkasa Afirka (BEAR) III, wani shiri na hadin gwiwa da hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) da Jamhuriyar Koriya suka yi.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan wayar da kan jama’a ma’aikatar ilimi ta jihar Kano Balarabe Abdullahi Kiru, yace aikin yana da nufin haɓaka ilimin fasaha da na sana’a a faɗin Afirka, tare da mai da hankali kan ƙarfafa tsarin ilimin fasaha da na sana’a da horo (TVET).
Aikin zai mayar da hankali ne kan harkar noma, tare da mai da hankali kan sarrafa kayan noma da sarrafa su bayan girbi.
A cewar Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda, shirin na BEAR III ya yi daidai da ajandar Gwamna Abba Kabir Yusuf na inganta shirye-shiryen koyon sana’o’i don dogaro da kai.
Ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kano za ta ci gaba da hada gwiwa da hukumar UNESCO da kasar Koriya ta Kudu domin bunkasa koyar da sana’o’i a makarantun furamare da na gaba da sakandare a fadin jihar.
Darakta a ma’aikatar ilimi ta tarayya Dr. (Mrs) M.A Olodo ta jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano domin gudanar da taro da masu ruwa da tsaki dangane da aiwatar da shirin na BEAR III.
Ta ba da tabbacin cewa ƙungiyar za ta yi amfani da mafi kyawun lokacin da ya rage don cimma manufofin aikin.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, an gina aikin na BEAR III akan ginshikai guda uku: sanya aikin ya dace da bukatun kasashe masu cin gajiyar shirin, da inganta TVET da ake bayarwa, da kuma kyautata fahimtarsa a tsakanin matasa.
Za a gudanar da aikin a kasashe hudu na yammacin Afirka: Najeriya, Ghana, Cote d’Ivoire, da Saliyo.
Rel/ Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
Gwamna Zulum ya nuna jin dadinsa ga kwamishinonin biyu, tare da yi musu fatan alheri a cikin ayyukansu na gaba.
Sai dai ya sanar da nadin Engr. Mohammed Habib da Ibrahim Hala Hassan domin maye gurbin kwamishinonin biyu da aka sauke.
A halin da ake ciki, Gwamna Zulum ya kuma amince da nadin Farfesa Yusuf Gana Balami a matsayin Shugaban Hukumar Ilimin Sakandare ta Jihar Borno.
Balami, Farfesa a fannin ilimi, ya fito ne daga Hawul da ke kudancin jihar.
Zulum ya taya Balami murna tare da bukatar sa da ya yi amfani da shekarunsa na gogewa a fannin ilimi, a matsayin shugaba a bangaren gudanarwa da karantarwa wajen sake fasalin ilimin sakandare a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp