Aminiya:
2025-07-31@17:52:04 GMT

Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina

Published: 26th, March 2025 GMT

Gidauniyar Daily Trust (DTF) tare da haɗin gwiwar ƙungiyar WRAPA, Hamu Legal, da Bahama Chambers, sun biya tarar fursunoni 21 domin su samu damar fita daga gidajen gyaran hali a Jihohin Kaduna da Katsina.

A Kaduna, an ’yanta mutum 17 bayan da DTF da abokan aikinta suka biya tarar su har Naira miliyan biyu da dubu dari biyu.

Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa

Laifuffukan da aka yanke musu hukunci sun haɗa da sata, shiga da karɓar kayan sata.

Da yake jawabi ga waɗanda aka fitar, Daraktan Gidauniyar Daily Trust, Dokta Theophilus Abbah, ya ce manufar shirin shi ne rage cunkoson fursunoni da kuma bai wa waɗanda suka aikata ƙananan laifuka damar gyara rayuwarsu.

Ya kuma yi kira a gare su da su koma cikin al’umma su rayu cikin gaskiya da riƙon amana.

Jami’in shirin WRAPA, Paul Adama, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da bayar da tallafi a ɓangaren shari’a domin ganin irin wannan aiki ya ci gaba da gudana.

A Jihar Katsina kuwa, an ‘yanta fursunoni huɗu cikin haɗin gwiwa tsakanin WRAPA da DTF.

Ɗaya daga cikinsu wani matashi ne daga Batsari wanda ya rasa iyayensa a harin ’yan bindiga kuma aka kama shi da laifin satar Naira 60,000.

Ya ka sa biyan tarar Naira 10,000 da diyyar Naira 60,000 har sai da Gidauniyar Daily Trust ta biya masa.

Mataimakin Konturola na Katsina, Lawal Talle, ya jinjina wa Gidauniyar Daily Trust da abokan haɗin gwiwarta bisa wannan taimako.

Sai dai kuma ya gargaɗi waɗanda aka ’yanta da su guji komawa aikata laifuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yanci gidauniya Gidauniyar Daily Trust

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.

A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.

’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.

Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.

Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci