Aminiya:
2025-06-15@09:46:48 GMT

Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina

Published: 26th, March 2025 GMT

Gidauniyar Daily Trust (DTF) tare da haɗin gwiwar ƙungiyar WRAPA, Hamu Legal, da Bahama Chambers, sun biya tarar fursunoni 21 domin su samu damar fita daga gidajen gyaran hali a Jihohin Kaduna da Katsina.

A Kaduna, an ’yanta mutum 17 bayan da DTF da abokan aikinta suka biya tarar su har Naira miliyan biyu da dubu dari biyu.

Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa

Laifuffukan da aka yanke musu hukunci sun haɗa da sata, shiga da karɓar kayan sata.

Da yake jawabi ga waɗanda aka fitar, Daraktan Gidauniyar Daily Trust, Dokta Theophilus Abbah, ya ce manufar shirin shi ne rage cunkoson fursunoni da kuma bai wa waɗanda suka aikata ƙananan laifuka damar gyara rayuwarsu.

Ya kuma yi kira a gare su da su koma cikin al’umma su rayu cikin gaskiya da riƙon amana.

Jami’in shirin WRAPA, Paul Adama, ya tabbatar da cewa za su ci gaba da bayar da tallafi a ɓangaren shari’a domin ganin irin wannan aiki ya ci gaba da gudana.

A Jihar Katsina kuwa, an ‘yanta fursunoni huɗu cikin haɗin gwiwa tsakanin WRAPA da DTF.

Ɗaya daga cikinsu wani matashi ne daga Batsari wanda ya rasa iyayensa a harin ’yan bindiga kuma aka kama shi da laifin satar Naira 60,000.

Ya ka sa biyan tarar Naira 10,000 da diyyar Naira 60,000 har sai da Gidauniyar Daily Trust ta biya masa.

Mataimakin Konturola na Katsina, Lawal Talle, ya jinjina wa Gidauniyar Daily Trust da abokan haɗin gwiwarta bisa wannan taimako.

Sai dai kuma ya gargaɗi waɗanda aka ’yanta da su guji komawa aikata laifuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yanci gidauniya Gidauniyar Daily Trust

এছাড়াও পড়ুন:

ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2

Abdulazeez pleaded not guilty to the two-count charge. Abdulazeez ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da su biyu.

Bayan rokon da ta yi, lauyan ICPC, Hamza Sani, ya bukaci kotun ta dage sauraron karar zuwa ranar 13 ga watan Yuni, 2025, domin masu gabatar da kara su gabatar da shaidu.

Sai dai daga baya kotun ta ba da ranar sannan ta dage sauraron karar zuwa ranar 20 ga watan Yunin 2025 domin sauraron karar.

Lauyan wanda ake tuhuma ya nemi a ba shi belin, wanda ICPC ba ta yi adawa da shi ba.

Mai shari’a Iheabunke ya bayar da belinta a kan kudi naira miliyan 10, tare da mutane biyu da za su tsaya mata.

Ya ce dole ne wadanda ake kara su mallaki kadarorin da ke karkashin ikon kotun, sannan su mika takardun mallakar asali ga magatakardar kotun don tantancewa, sannan wanda ake kara ya sanar da kotu a hukumance kafin tafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa