HausaTv:
2025-06-15@22:36:18 GMT

Karancin Man Fetur A Jamhuriyar Nijar Yana Damun ‘Yan Kasa

Published: 14th, March 2025 GMT

An kusa shiga mako guda daga lokacin da aka fara fuskantar karancin mai a gidajen man fetur da hakan ya jefa masu ababan hawa cikin damuwa.

Rabon man fetur da kamfanin SONIDEP yake yi bai wadatar da masu abubuwan hawa ba, yana kuma kawo cikas a harkokinsu na yau da kullum.

Da akwai dalilai da dama da su ka haddasa karancin man fetur din, sai dai al’ummar kasar suna son ganin mahukunta sun fito fili sun yi musu bayanin abinda yake faruwa.

Wani mazaunin birnin Yemai Assoumane Hamadou suley ya fada wa manema labaru cewa; Ba mu da cikakken bayani akan abinda yake faruwa, domin mahukanta da ya kamata su fito su yi bayani, ba su yin hakan.

Su kuwa matukan motocin Tasi (SYNCTAXITU), cewa su ka yi, ya kamata gwamnati ta kara yawan man fetur da ake hakowa a kowace rana.

Babban sakataren kungiyar matuka Tasi din Agali Ibrahim cewa ya yi, “ Idan aka fada mana cewa da akwai manyan motocin jigilar man fetur 25 da ake bai wa birnin Niamey, to abinda zan fada musu shi ne cewa bai isa ba.”

Haka nan kuma ya yi ishara da fasakwaurin man fetur din da ake yi da yana daga cikin dalilin karancinsa da ake fuskanta.

Da akwai shirin kara yawan tankokin mai daga 25 zuwa 100 da za a rika bai wa babban birnin ka kowace rana.

Ba kasafai ake shiga irin wannan yanayin ba a jamhuriyar Nijar wacce take da arzikin mamn fetur da aka fara hako shi tun a wajajen 2011.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bude kofofin wuta a kan haramtacciyar kasar Isra’ila ta hanyar mayar da martani kan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasarta

Iran ta bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya a matsayin mayar da martani ga mummunan zaluncin da suka kaddamar kan lardunan Iran da dama, wanda ya yi sanadiyyar shahadan mutane da dama da jikkata.

Bayan da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Wajibi ne gwamnatin mamayar Isra’ila ta jira mummunan hukunci mai tsanani da kuma makoma mai daci kan abin da aikata, kuma bayan da sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci Manjo Janar Muhammad Pakpour ya bayyana cewa: Sojojin kasar Iran za su bude kofofin jahannama kan kisan yara kanana, Iran ta fara kaddamar da hare-haren daukan fansa mai suna “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda ta harba makamai masu linzami na ballistic da hypersonic kan yankuna daban daban na haramtacciyar kasar Isra’ila.

A cewar faifan bidiyo da aka wallafa, hakika Iran ta kai hare-hare da makamai masu linzami kan tsakiyar birnin Tel Aviv da kuma cibiyoyi da dama na soji da sansanonin sojin saman haramtacciyar kasar Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai