Sojoji sun ceto mutum 7 daga hannun ’yan bindiga a Filato
Published: 14th, March 2025 GMT
Jami’an tsaro a Jihar Filato, sun ceto mutum bakwai da ’yan bindiga suka sace.
An gano mutanen a yankin Ganawuri, da ke Ƙaramar Hukumar Riyom, bayan da sojojin Operation SAFE HAVEN (OPSH) suka kai farmaki maɓoyar ’yan bindigar.
Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-RufaiAn gudanar da aikin ceton ne a matsayin wani ɓangare na Operation LAFIYAN JAMA’A, wanda ke da nufin tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Mai magana da yawun rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya bayyana cewa sojojin sun samu bayanan sirri cewa an ɓoye wasu mutane da aka sace a kusa da hanyar Jos zuwa Ganawuri.
“Yayin farmakin, sojojinmu sun yi arangama da ‘yan bindigar, amma sun tsere bayan sun fuskanci ruwan wuta.
“Daga nan, sojojin suka bi sahu suka kuma ceto mutum bakwai da maharan suka sace,” in ji Manjo Zhakom.
An bayyana sunan mutanen da aka ceto, waɗanda dukkaninsu ‘yan asalin Jihar Bauchi ne: Sale Umar, Muhammadu Inusa, Abdullahi Abdulrasaq, Abdulsalam Muhammad, Muhammad Hamisu, Ibrahim Maradu, da Saidu Sani.
Sojojin sun kuma gano wata jaka mai ɗauke da bargo da kaya da ‘yan bindigar suka bari.
Sun yi wa mutanen da suka ceto tambayoyi don taimakawa musu da bayanan da za su sa a kama ‘yan bindigar da suka tsere.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan bindigar
এছাড়াও পড়ুন:
Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun sanar a cikin wani sako mai cike da alhini da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun IRGC wanda ya yi shahada da asubahin ranar Juma’ar nan yayin wani hari na ta’addanci” da gwamnatin sahyoniyawan ta kai kan hedkwatar rundunar.
Hukumar soji tana jinjinawa wannan babban kwamandan da aka gabatar a matsayin babban jigo wajen kare manufofin juyin juya halin Musulunci na Iran, tare da yin alkawarin mayar da martani mai tsauri ga makiya.
Ga yadda sanarwar IRGC ta kasance :
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
A cikin bakin ciki da radadi muna sanar da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci, da da wasu mukarabansa, a lokacin harin ta’addancin da gwamnatin sahayoniya ta kai a safiyar wannan ranar ta Juma’a akan hedkwatar IRGC yayin da suke gudanar da muhimmin aiki na tsaron kasa.
Muna mika ta’aziyyarmu ga Jagoran juyin juya halin Musulunci kuma babban kwamandan sojojin kasar, Imam Khamenei, da iyalan duk wadanda abun ya shafa.
Duk da wannan harin na dabbanci, muna tabbatar wa al’ummar Iran masu daraja cewa, har yanzu rundunar sojojin Iran a shirye suke don maida martani ga gwamnatin sahyoniyawan.
Nan ba da jimawa ba za a isar da cikakken bayani kan halin da ake ciki biyo bayan harin na makiya da kuma matakin da za a dauka na hukunta su.
Haka zalika kafofin yada labarai na Iran sun rawaito shahadar babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Mohammad Hossein Baqeri.
Shi ma Manjo Janar Baqeri ya yi shahada a wani harin ta’addanci da gwamnatin sahyoniya ta kai birnin Tehran a safiyar yau Juma’a.