Sojoji sun ceto mutum 7 daga hannun ’yan bindiga a Filato
Published: 14th, March 2025 GMT
Jami’an tsaro a Jihar Filato, sun ceto mutum bakwai da ’yan bindiga suka sace.
An gano mutanen a yankin Ganawuri, da ke Ƙaramar Hukumar Riyom, bayan da sojojin Operation SAFE HAVEN (OPSH) suka kai farmaki maɓoyar ’yan bindigar.
Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai Da amincewar Buhari na fice daga jam’iyyar APC — El-RufaiAn gudanar da aikin ceton ne a matsayin wani ɓangare na Operation LAFIYAN JAMA’A, wanda ke da nufin tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Mai magana da yawun rundunar, Manjo Samson Zhakom, ya bayyana cewa sojojin sun samu bayanan sirri cewa an ɓoye wasu mutane da aka sace a kusa da hanyar Jos zuwa Ganawuri.
“Yayin farmakin, sojojinmu sun yi arangama da ‘yan bindigar, amma sun tsere bayan sun fuskanci ruwan wuta.
“Daga nan, sojojin suka bi sahu suka kuma ceto mutum bakwai da maharan suka sace,” in ji Manjo Zhakom.
An bayyana sunan mutanen da aka ceto, waɗanda dukkaninsu ‘yan asalin Jihar Bauchi ne: Sale Umar, Muhammadu Inusa, Abdullahi Abdulrasaq, Abdulsalam Muhammad, Muhammad Hamisu, Ibrahim Maradu, da Saidu Sani.
Sojojin sun kuma gano wata jaka mai ɗauke da bargo da kaya da ‘yan bindigar suka bari.
Sun yi wa mutanen da suka ceto tambayoyi don taimakawa musu da bayanan da za su sa a kama ‘yan bindigar da suka tsere.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan bindigar
এছাড়াও পড়ুন:
Riza’i: Babu Hannun Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
Kakakin kwamitin tsaron kasa a majalisar shawarar musulunci ta Iran ya bayyana cewa; ” Ya zuwa yanzu ba za mu iya yin hukunci akan dalilan da su ka haddasa fashewar abubuwa a tashar ruwa ta Shahid Raja’i ba, amma za mu iya cewa babu hannu waje a ciki.
Kakakin kwamitin tsaron kasar ta Iran Ibrahim Rizai wanda ya halarci taron da aka yi a Majalisa akan fashewar da aka samu a tashar ruwan ta shahid Raja’i, ya kuma kara da cewa; Fahimtata da abinda na ji daga abokan aikina dangane da abinda ya faru a tashar ruwa ta Shahid Raja’i, da kuma rahotannin da su ka iso mana, shi ne cewa abinda ya farun ba shi da alaka da waje.”
A ranar Asabar da ta gabata ne dai wasu abubuwa su ka fashe a tashar ruwa ta Shahid Raja’i dake Bandar Abbas a kudancin Iran, wanda ya haddasa asarar rayuka da kuma jikkatar daruruwan mutane.
An bude kwamitin bincike domin gano hakikanin abinda ya faru a tashar da kuma haddas fashewar abubuwan masu karfi.