Shuwagabannin kasashen Turai, sun amince da kara kudade mai yawa a bnaren tsaro da kuma tallafawa kasar Ukraine, a yakin da take yi da kasar Rasha, saboda janyewar Amurka dukkan taimakon da take bawa kasar ta Ukraine.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar taron shuwagabannin kasashen na Turai, sun zuba kudade dalar Amurka biliyon $860 (Euro 800bn) don karfafa kasashen Turai da kuma Ukrania.

Shugaban kungiyar ta EU Ursula von de Leyen yace a karon farko tsaron kasashen yake komawa kansu bayan da Amurka ta dauki nauyin hakan tun bayan yakin duniya na II.

A halin yanzu gwamnatin kasar Amurka tace ba zata ci gaba da kashewa wadannan kashe kudade don tsarunsu ta kungiyar tsaro ta Nato ba.

Shugaban yace EU zata gaggauta tattarawa harkokin tsaron kasashen EU saboda bunkatashi da sauri.

De Leyen ya kara da cewa ba zai yu a tattauna dangane da yakin a Ukraine ba tare da ita kasar Ukraine ko kasashen turai ba. Kasashen kungiyar 26 daga cikin 27 sun amince da wannan matin da suka fara dauka in banda kasar Hungary.

Volodomir Zelesky na kasar Ukraine ya isa taron kafin a fara shi a birnin Brssels, ya kuma godewa kasashen na Turai kan wannan kokarin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana

Gabanin tafiyar shugaban kasar Sin Xi Jinping birnin Astana na kasar Kazakhstan, inda zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, an kaddamar da bikin gabatar da jerin shirye-shiryen shirye-shiryen telebijin da fina-finai, na babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG na shekarar 2025 a birnin Astana.

Za a gabatar da shirye-shiryen CMG guda 12, ciki har da alakar dake tsakanin shugaba Xi Jinping da al’adun kasar Sin, da hanyar zamanintar da kasa mai salon kasar Sin na musamman da sauransu, a manyan kafofin watsa labaru na kasashen Kazakhstan, da Kyrgyzstan, da Tajikistan, da Turkmenistan, da Uzbekistan da dai sauransu.

Shugaban gidan CMG Shen Haixiong ya bayyana cewa, a ta bakin shugaba Xi Jinping, kasar Sin kyakkyawar abokiya ce ta kasashen tsakiyar Asiya, don haka ya kamata a kara yin kokari wajen raya makomar bai daya ta Sin da kasashen tsakiyar Asiya. Kuma kafar CMG ta yi hadin gwiwa tare da kafofin watsa labaru na kasashen tsakiyar Asiya, wajen gabatar da shirye-shirye, don sa kaimi ga aiwatar da ayyukan da aka cimma, a taron koli na Sin da tsakiyar Asiya na shekarar 2023, da kara gudanar da mu’amalar al’adu, da sada zumunta a tsakaninsu bisa manufofin da shugaba Xi ya gabatar. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki