Leadership News Hausa:
2025-05-01@04:24:47 GMT

Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

Published: 7th, March 2025 GMT

Bukatar Kafa Dokar-ta-baci Kan Yaduwar Jabun Magunguna

A kasuwar Ariaria da ke Aba, NAFDAC, sun gano jabun magunguna da kudinsu ya kai na miliyoyin Naira.

Bugu da kari, a kasuwar Idumota da ke a jihar Legas, NAFDAC sun garkame Shanguna sama da 3,000 bayan sun gano Shagunan shake da jabun magunguna.

A kasuwar kan Gadar Onitsha, nan ma Hukumar ta sun kama manyan motoci goma shake da jabun magungana, inda a bayan kamen dilolin magungunan suka yi yunkurin bai wa jami’an na NAFDAC cin hancin Naira miliyan 135.

Har ila yau, a kasurgumar kasuwar Cemetery da ke Aba, nan ma NAFDAC ta kama tare da kwace jabun magunguna da kudinsu ya kai na sama da Naira miliyan biyar.

Bisa batun gaskiya, irin wannan bakar hada-hadar jabun magunguna, ya wuce maganar alkaluma, domin kuwa, abinda yafi dacewa, shi ne, yankewa irin masu wannan bakar harkalar hukuncin ta hanyar rataye su, duba da yaddda suka kara jefa rayuwar marasa lafiya a cikin wata ukuba ta hanyar sayar da jabun magunguna.

Abinda ya kara jefa fargaba a zukakan jama’a ne, shi ne, kan irin hanyoyin da irin wadannan bata garin ke bi wajen sarrafa jabun magungunan, musamman ganin yadda suke da kayan aikin da suke sake sarrafa magungunan da suka riga suka lalace.

Kazalika, a wani gwaji da NAFDAC kan mangunan yara, da wadannan bata garin ke sarrafawa suke kuma sayar da shi, kan farashi mai sauki, NAFDAC bata iya gano wani abu da ba daidai ba.

Wannan rashin iya ganowar na NAFDAC ya nuna yadda sarrafa magungunan na jabu, sun jima suna yin sanadiyar mutuwar yara, ba tare da yin amfani da bakin Bindiga ba.

Wannan matsalar dai, ba wai kawai ta tsaya kan daidaikun ‘yan kasuwa masu sarrafa jabun magungunan bane, domin abu ne, da ya karade daukacin miyagun masana’tun da ke da ke sarrafa jabun, inda suka fakewa a matsayin Shaguna suna cikin Karensu babu babbaka ciki har da sarrafa jabun magunguna na yakar cuta mai karya garkuwar jiki.

A yayin samamane na NAFDAC, sama da haramtattun masana’antu 240 da ake sarrafa jabun magunguna aka bankado a kasuwar Cemetery.

A ra’ayin mu wadannan matakan da aka dauka na kai samame a kasuwannin bai isa ba, duba da cewa, hukuncin shigo da kwayar maganin Tramadol zuwa cikin kasar nan ta haramtacciyar hanya, shi ne, kodai yin shekaru biyar a gidan gyran hali ko kuma biyan tararar Naira 250,000, domin kuwa dole mu mayar da hankali wajen kare kiwon lafiyar yan kasar nan.

Mojisola Adeyeye, Darakta Janar ta kasa ta Hukumar NAFDAC, ta bukaci da a rinka yanke hukuncin kisa ga masu sarrafa jabun magunguna, duba da yadda suke jefa rayuwar alumma a cikin matsala da kuma jefa tsarin kiwon lafiya a cikin barazana.

Yawan samun irin wadannan kasuwannin na sarrafa jabun magungunnan duk da kokarin da NAFDAC ke kan yin a rage sarrafa jabun magungunan akalla zuwa kaso biyar a cikin dari a 2025, hakan na ci gaba da zama wani babban kalubale ga hukumar, musamman duba da yadda ake ci gaba da samun karuwar a kasar.

Wani abin bakin ciki shi ne, yadda halastatun kungiyoyin dilolin sarrafa magunguna kamar irin su, EKUMI Plaza Patent Medicine, suma suka bi sahu wajen shiga kazamar hanyar ta hada-hadar kasuwancin jabun magunguna da suka kai na Naira miliyan 50.

Karafafa yakar wannan lamarin bai wadatar ba, domin kuwa kamata ya yi a yiwa fannin rabar da magunna na kasar nan garanbawul baki daya.

Ci gaba da samun wanzuwar irin wadannan kasuwannin na sayar da jabun magunguna na kara haifar da gibi a bangaren tsarin kiwon lafiyar kasar.

Ya zama wajbi Gwamnatin Tarayya ta sake yin nazari kan bayar da takardun fito na shigo da magunguna cikin kasar, musamman domin a tallafawa halastattun masana’atun cikin gida da ke sarrafa magungunan.

Ya kuma kamata a kara karfafa shirin Inshorar kiwon lafiya na kasa NHIS, wanda hakan zai taimaka a rinka samar da ingantatun magunguna kuma a cikin farashi mai sauki, wanda hakan kuma zai sanya, durkushewar bakar kasuwar ta sayar da jabun magunnan a kasar.

Kazalika, akwai bukatar a rinka ilimantar da alummar gari kan illar irin wadannan jabun magungunan.

Bai kamata bangaren Shari’a ya rinka yin hukunci mai sauki ga masu wannan dabi’ar ba, musamman duba da yadda kawai irin masu wannan dabi’ar da suka shiga hannun hukuma ake cin su tara ‘yar kadan.

Dole kutuna sun tilatsa tsauraran hukunci, ciki har da yanke hukunci zaman gidan Yari da kuma yanke hukuncin haramtawa wadanda aka kama suna sarrafa jabun magunguna kara yin duk wata sana’a da ta shafi sarrafa magunguna.

Yawon da irin wadannna jabun magungunan a cikin alumma, tamkar yankewa iyalai hukuncin kisa ne.

Bugu da kari, ya zama wajbi daukacin ‘yan Nijeriya su tashi tsaye mu yi aiki tukuro domin kawo karshen wannan bakar dabi’ar, mu kuma jajirce har sai mun ga an a sayar da ingantatun magunguna a kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: sarrafa jabun magunguna sarrafa magunguna irin wadannan

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA

Shugaban hukumar makamshin Nujkliya ta MDD ya zanda da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi kan al-amuran da suka shafi shirin nukliyar kasar Iran da kuma tattaunawar da ake gudana tsakanin ta da Amurka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a tattaunawa ta wayar tarho tsakanin jami’an guda biyu a jiya Lahadi, Grossi shugaban IAEA ya bayyana cewa ya ji dadin yadda JMI ta zabi tattaunawa da AMurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya. Ya kuma bayyana cewa hukumarsa a shirye take ta gabatar da duk wani taimakon da JMI take bukata a yayin tattaunawar.

A nashi bangaren Abbas Araqchi ya bayyana cewa kasar Iran a shirye take ta bada hadin kai ga hukumar ta IAEA kamar yadda yarjeniyar NPT take bukata da kuma dokokin kasa da kasa.

Abbas ya fada masa inda aka kai ya zuwa yanzu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, a biranen Mascat na kasar Omman da kuma Roma na kasar Italiya.

Ya zuwa yanzu dai kasashen biyu sun gudanar da taro har sau uku dangane da shirin Nukliyar kasar ta Iran, kuma bangarorin biyu sun bayyana amincewarsu da yadda tattaunawar take tafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Cinikayyar Hidima Ta Kasar Sin Ta Matukar Bunkasa A Rubu’in Farko Na Nana
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar