A wani yunkuri na bunkasa sana’o’in hannu da kuma karfafa wa masu bukata ta musamman, wata kungiya mai zaman kanta mai suna Women Farmers Advancement Network (WOFAN) ta kaddamar da wata cibiyar kasuwanci ta mata masu sarrafa kayayyaki tare da baiwa masu bukatar su 450 a yankin Karfi.

Wannan yunƙurin na da nufin ƙarfafa su 450 da kayan aikin farawa, wanda zai ba su damar yin aiki mai daraja da riba.

Da take jawabi a wajen taron, Daraktar Hukumar WOFAN-ICON2, Dakta Salamatu Garba, wadda ta samu wakilcin jami’in kula da ofishin na Kano, Alhaji Dayyabu Abubakar, ta jaddada cewa cibiyar kasuwanci za ta baiwa mata damar kula da harkokin kasuwancinsu da kuma amfani da dabarun tattaunawa da suka samu ta hanyar WOFAN.

Ta bayyana cewa, wannan shiri zai karfafawa mata ta hanyar ba su ikon sarrafa albarkatunsu, da kara samun riba, da kuma fadin albarkacin bakinsu kan batutuwan da suka shafe su.

Ta kara da cewa shirin ya yi daidai da manufofin shirin WOFAN-ICON2 a karkashin gidauniyar Mastercard, wanda ke kokarin samar da ayyukan yi mai dorewa ga matasa, mata, da masu bukata ta musanna a jihohi goma na Najeriya. Wanda shi ne shirin shekara biyar.

“Cibiyar kasuwancin Karfi ita ce irinta ta biyu a karamar hukumar Kura, bayan da aka kafa irin wannan wurin a kasuwar Kura. Kasuwar Kura, daya ce daga cikin manyan kasuwannin da dake Kano, tana sayar da hatsi sama da tireloli 500 a kullum zuwa wurare daban-daban a ciki da wajen Najeriya.”

Hakimin Karfi, Alhaji Magaji Shehu wanda Jamilu Magaji ya wakilta ya taya wadanda suka ci gajiyar shirin murna, inda ya bayyana cewa shirin ba wai kawai zai amfanar da jama’a ba, zai kuma yi tasiri ga al’umma baki daya.

Wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Safiya Isah, Safiya Isah Kura, Rakiya Rabi’u, Haruna Sule Karfi da Sule Shehu sun nuna jin dadinsu da tallafin tare da ba da tabbacin za su yi amfani da kudaden cikin adalci.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, cibiyar kasuwancin ta kunshi shaguna guda uku: daya yana aiki a matsayin ofishi da mambobin kungiyar za su tattauna matsalolinsu da dabarun kasuwanci a cikin kasuwar Karfi, yayin da sauran biyun kuma aka kebe su domin gudanar da harkokin kasuwanci.

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Karfi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala

Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.

Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.

Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.

Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.

El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.

A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.

Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.

Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.

Yadda aka yi muƙabala tsakanin Shehi Tajul Izzi da Maidubun Isa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa