Wata Kungiya Mai Zaman Kanta Ta Ba Masu Bukata Ta Musamman Su 450 Tallafi a Kano
Published: 6th, March 2025 GMT
A wani yunkuri na bunkasa sana’o’in hannu da kuma karfafa wa masu bukata ta musamman, wata kungiya mai zaman kanta mai suna Women Farmers Advancement Network (WOFAN) ta kaddamar da wata cibiyar kasuwanci ta mata masu sarrafa kayayyaki tare da baiwa masu bukatar su 450 a yankin Karfi.
Wannan yunƙurin na da nufin ƙarfafa su 450 da kayan aikin farawa, wanda zai ba su damar yin aiki mai daraja da riba.
Da take jawabi a wajen taron, Daraktar Hukumar WOFAN-ICON2, Dakta Salamatu Garba, wadda ta samu wakilcin jami’in kula da ofishin na Kano, Alhaji Dayyabu Abubakar, ta jaddada cewa cibiyar kasuwanci za ta baiwa mata damar kula da harkokin kasuwancinsu da kuma amfani da dabarun tattaunawa da suka samu ta hanyar WOFAN.
Ta bayyana cewa, wannan shiri zai karfafawa mata ta hanyar ba su ikon sarrafa albarkatunsu, da kara samun riba, da kuma fadin albarkacin bakinsu kan batutuwan da suka shafe su.
Ta kara da cewa shirin ya yi daidai da manufofin shirin WOFAN-ICON2 a karkashin gidauniyar Mastercard, wanda ke kokarin samar da ayyukan yi mai dorewa ga matasa, mata, da masu bukata ta musanna a jihohi goma na Najeriya. Wanda shi ne shirin shekara biyar.
“Cibiyar kasuwancin Karfi ita ce irinta ta biyu a karamar hukumar Kura, bayan da aka kafa irin wannan wurin a kasuwar Kura. Kasuwar Kura, daya ce daga cikin manyan kasuwannin da dake Kano, tana sayar da hatsi sama da tireloli 500 a kullum zuwa wurare daban-daban a ciki da wajen Najeriya.”
Hakimin Karfi, Alhaji Magaji Shehu wanda Jamilu Magaji ya wakilta ya taya wadanda suka ci gajiyar shirin murna, inda ya bayyana cewa shirin ba wai kawai zai amfanar da jama’a ba, zai kuma yi tasiri ga al’umma baki daya.
Wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Safiya Isah, Safiya Isah Kura, Rakiya Rabi’u, Haruna Sule Karfi da Sule Shehu sun nuna jin dadinsu da tallafin tare da ba da tabbacin za su yi amfani da kudaden cikin adalci.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, cibiyar kasuwancin ta kunshi shaguna guda uku: daya yana aiki a matsayin ofishi da mambobin kungiyar za su tattauna matsalolinsu da dabarun kasuwanci a cikin kasuwar Karfi, yayin da sauran biyun kuma aka kebe su domin gudanar da harkokin kasuwanci.
KHADIJAH ALIYU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Karfi
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Gwamnan Jihar Filato, Barr. Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa babu wata ƙaramar hukuma a cikin jihar da ƴan ta’adda ko ƴan bindiga ke da iko da ita. Ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ƴan jarida da aka gudanar a sabon gidan gwamnati da ke Little Rayfield, Jos, a ranar Talata.
Gwamna Mutfwang ya ce gwamnatinsa ta ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar tsaro, musamman ta hanyar farfaɗo da rundunar tsaron cikin gida ta jihar wato Operation Rainbow, domin tallafa wa sauran hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ana Ci Gaba Da Alhinin Mutuwar Malam Adamu Fika Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A FilatoYa ƙara da cewa, gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen ganin an dawo da zaman lafiya a sassan jihar da rikice-rikicen ƙabilanci ko na addini suka taɓa. Ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin tsaro da shugabannin gargajiya domin tabbatar da fahimtar juna da daidaiton al’umma.
Gwamnan ya sake jaddada buƙatar kafa ƴansandan jiha, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen rage matsalolin tsaro a faɗin Nijeriya. Ya ce kafa ƴansandan jiha zai bai wa gwamnatocin jihohi damar yin tsari da ɗaukar matakan da suka dace da yanayin tsaron yankunansu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp