Mijina bai hana ni waƙa ba sai dai… – Fa’iza Badawa
Published: 5th, March 2025 GMT
Fa’iza Muhammad wacce aka fi sani da Fa’iza Badawa, daya ce daga cikin mawakan Kannwood.
Ita ta yi wakar fim din Oga Abuja, daya daga cikin finafinan suka yi tashe, ya kuma fito da basirar mawakiyar.
Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata Mai barkwanci ya yi kuskuren liƙe bakinsa da sufa-giluKasancewar ta yi aure, mutane sun ɗauka ta daina harkar waƙa baki ɗaya.
Yaushe kika yi aure?
Na yi aure ne a ranar 8 watan Afrilun shekar 2017, kuma ina zaune lafiya da mijina da kuma haihuwa daay da Allah Ya bamu, kuma aure ne na so ada kauna da kuma kyakkyawar kulawa. Kuma yana taimaka min tare da goya min baya a abubuwan ada na ke yi.
Shin gaskiya ne cewa auren ne ya hana ki ci gaba da waka?
Ba gaskiya ba ne. Har yanzu ina yin waka, kuma duk wasu manya-manya da ke wannan sana’a sun san har yanzu ina yin waka saboda muna aiki tare.
Duk lokacin da suke bukatar aiki da ni, su kan kira ni ko kuma su kira mijina tare neman izininsa na mu yi aiki ko aika masa sako zuwa gare ni.
Mu mawaka a bayan fage muke, ba ganinmu ake yi ba, sai dai a ji muryoyinmu wanda da shi a ke gane mu, da kuma cewa, yawancinmu mawaka mata da zarar mun yi aure sai mu daina aiki, shi ya sa da yawa suka dauka nima na daina waka.
A lokuta na kan yi wa abokan aikina bayani cewa, ina nan, na kuma ci gaba da sana’ata ta waka a wannnan masana’antar tamu.
Shin ko yaya ki ke tafiyar da wannan sana’a a yanzu da kina matar aure?
Wani tsari na fito da shi la’akari da tsarin addinina da kuma kula da matsayina a inda na kan bukaci duk mai son in yi mi shi waka da ya je ya gama rubuta wakarsa, ya kuma gama shiririnsa da wurin daukar murya.
Idan ya yi hakan, sai in nemi a sa min ranata ni kadai da zan je in yi nawa baitukan ko kuma dora murya. Inda na gama sai su ci gaba da sauran wadanda za su yi da su.
Kuma ya kamata ka sani cewa, ba ni kadai ce na ke da aure ba, na kuma ke waka, domin muna da yawa a yanzu fiye da yadda ka ke tunani.
Ka ga da akwai Zuwairiya Isma’ila, da Murja Baba, da Naja’atu Ta’Annabi, da Maryam A Baba, da Jamila Sadi, da Zainab Diamond, da Sa’a Bocal, da kuma Sa’a Nazifi Asnanic. Da sauransu.
Wane kalubale ne kike fuskanta a matsayinki na mawakiya kuma matar aure?
Ni babu wata matsala da na ke fuskanta a matsayina na matar aure kuma mai sana’ar waƙa musamman ma a gidan mijina.
Domin akwai kyakkyawar fahimta tsakanina da shi, bayan so da kauna, ya na bani sharwari tare da tallafa min a duk al’amurana ciki har da wannan sana’a ta waka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fa iza Badawa kannywood Waƙa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
Mai kuɗin Afrika kuma Shugaban Matatar Mai ta Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya zargi wasu manyan masu harkar mai da shirya maƙarƙashiya domin kashe matatarsa.
Ɗangote ya yi zargin cewa miyagun ’yan kasuwan suna ƙoƙarin kashe matatar mansa mai darajar dala biliyan 20, kamar yadda aka kashe masana’antar tufafi ta ƙasar.
Ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Legas yayin bikin cika shekara ɗaya da fara samar da fetur a matatar, inda ya ce tafiyar ta kasance cike da ƙalubale tun daga farko.
“A gaskiya tafiyar shekara ɗaya da ta wuce ta yi mana matuƙar wuya. Mun zo mu sauya tsarin kasuwancin man ƙasa. Amma wasu na ganin mun raba su da hanayar cin abinci bakinsu,” in ji shi.
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati BaYa ci gaba da cewa, “Amma abin da muka yi shi ne mun sa Najeriya da nahiyar Afirka gaba ɗaya su yi alfahari.”
Ɗangote ya ce matatar ta riga ta fitar da lita biliyan 1.8 na man fetur zuwa ƙasashen waje cikin watanni uku da suka gabata, sannan tana da isasshen ƙarfi wajen cika buƙatar cikin gida.
Ya ce tun daga fara aikin matatar a watan Satumbar 2024, dogayen layukan man fetur da suka fi shekaru 50 ana fama da su a Najeriya sun zama tarihi.
Ɗangote ya ƙara da cewa farashin fetur ya sauka daga kusan Naira 1,100 zuwa N841 a wasu jihohi, kuma da zarar sabbin motocin gas (CNG) masu dakon mai sun fara aiki a duk faɗin ƙasar, rage farashin zai fi tasiri.
Ya kuma bayyana cewa sabbin motocin CNG 4,000 za su samar da aƙalla ayyukan yi 24,000, ciki har da direbobi, makanikai da sauran ma’aikata.
“Ba mu kore kowa daga aiki ba, sai dai muna ƙara samar da ayyuka,” in ji shi.
Ɗangote ya zargi masu harkar mai da haɗa kai da ’yan kasuwa na cikin gida da na waje da ƙoƙarin hana nasarar matatar.
“Yadda aka hallaka masana’antar yadi, haka suke ƙoƙarin kashe matatar mu,” in ji shi.
A kan zargin cewa bai wadatar da ƙasa da fetur ba, sai ya mayar da martani da cewa: “Idan ba mu da ƙarfin samar da mai, me ya sa muke fitarwa zuwa ƙasashen waje?”
Ya kuma yi ba’a ga Ƙungiyar Ma’aikatan Mai (NUPENG) wadda ta ce rage farashin fetur na matatar Dangote “kyautar Girka ce.” Dangote ya ce: “Ko da kuwa kyautar Girka ce, ai kyauta ce, za ta kuma ci gaba da kasancewa.”
Ya jaddada cewa abin da Najeriya ke buƙata yanzu shi ne kare masana’antunta, domin ci-gaban tattalin arziki da kuma rage dogaro da shigo da kaya daga waje.