Aminiya:
2025-05-01@04:31:12 GMT

Mijina bai hana ni waƙa ba sai dai… – Fa’iza Badawa

Published: 5th, March 2025 GMT

Fa’iza Muhammad wacce aka fi sani da Fa’iza Badawa, daya ce daga cikin mawakan Kannwood.

Ita ta yi wakar fim din Oga Abuja, daya daga cikin finafinan suka yi tashe, ya kuma fito da basirar mawakiyar.

Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata Mai barkwanci ya yi kuskuren liƙe bakinsa da sufa-gilu

Kasancewar ta yi aure, mutane sun ɗauka ta daina harkar waƙa baki ɗaya.

Sai a hirarta da wakilinmu Ibrahim Musa Giginyu, Fa’iza ta ce ba haka ba ne.

Yaushe kika yi aure?

Na yi aure ne a ranar 8 watan Afrilun shekar 2017, kuma ina zaune lafiya da mijina da kuma haihuwa daay da Allah Ya bamu, kuma aure ne na so ada kauna da kuma kyakkyawar kulawa. Kuma yana taimaka min tare da goya min baya a abubuwan ada na ke yi.

Shin gaskiya ne cewa auren ne ya hana ki ci gaba da waka?

Ba gaskiya ba ne. Har yanzu ina yin waka, kuma duk wasu manya-manya da ke wannan sana’a sun san har yanzu ina yin waka saboda muna aiki tare.

Duk lokacin da suke bukatar aiki da ni, su kan kira ni ko kuma su kira mijina tare neman izininsa na mu yi aiki ko aika masa sako zuwa gare ni.

Mu mawaka a bayan fage muke, ba ganinmu ake yi ba, sai dai a ji muryoyinmu wanda da shi a ke gane mu, da kuma cewa, yawancinmu mawaka mata da zarar mun yi aure sai mu daina aiki, shi ya sa da yawa suka dauka nima na daina waka.

A lokuta na kan yi wa abokan aikina bayani cewa, ina nan, na kuma ci gaba da sana’ata ta waka a wannnan masana’antar tamu.

Shin ko yaya ki ke tafiyar da wannan sana’a a yanzu da kina matar aure?

Wani tsari na fito da shi la’akari da tsarin addinina da kuma kula da matsayina a inda na kan bukaci duk mai son in yi mi shi waka da ya je ya gama rubuta wakarsa, ya kuma gama shiririnsa da wurin daukar murya.

Idan ya yi hakan, sai in nemi a sa min ranata ni kadai da zan je in yi nawa baitukan ko kuma dora murya. Inda na gama sai su ci gaba da sauran wadanda za su yi da su.

Kuma ya kamata ka sani cewa, ba ni kadai ce na ke da aure ba, na kuma ke waka, domin muna da yawa a yanzu fiye da yadda ka ke tunani.

Ka ga da akwai Zuwairiya Isma’ila, da Murja Baba, da Naja’atu Ta’Annabi, da Maryam A Baba, da Jamila Sadi, da Zainab Diamond, da Sa’a Bocal, da kuma Sa’a Nazifi Asnanic. Da sauransu.

Wane kalubale ne kike fuskanta a matsayinki na mawakiya kuma matar aure?

Ni babu wata matsala da na ke fuskanta a matsayina na matar aure kuma mai sana’ar waƙa musamman ma a gidan mijina.

Domin akwai kyakkyawar fahimta tsakanina da shi, bayan so da kauna, ya na bani sharwari tare da tallafa min a duk al’amurana ciki har da wannan sana’a ta waka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fa iza Badawa kannywood Waƙa

এছাড়াও পড়ুন:

Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa

Wata koutun soja ta yanke wa wani jami’inta hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun sa da laifn kashe buduwarsa.

Kotun da ta zauna a Hedikwatar Runduna ta 82 da ke Enugu, ta yanke wa Private Adamu Mohammed hukuncin kisa kan laifin budurwar taas mai suna Hauwa Ali.

Da yake sanar da hukuncin, Shugaban kotun, Birgediya Sadisu Buhari, ya ce, “Kotun Soja ta Kasa ta yanke hukuncin cewa sojan da ake tuhuma, mai lamba 21NA/80/6365 Private Adamu Mohammed, an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa tuhumar kisan kai.”

Mukaddashin kakakin Rundunar, Jonah Unuakhalu, ya ce kwamitin kotun  ya cimma matsaya ɗaya bayan nazari mai zurfi na shaidu, tarihin aikin wanda ake tuhuma, da kuma roƙon sassauci daga lauyansa.

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno

Ya shaida wa manema labarai a Abuja cewa kotun sojan, ta kuma yanke wa wani Soja mai suna Private Abubakar Yusuf hukuncin ɗaurin shekaru 10 a kurkuku saboda samun sa da laifin fashi da makami a wani shahararren kantin sayayya a Enugu.

Ya kara da cewa an yanke wa waɗannan mutane biyu hukuncin ne bayan kammala shari’o’insu kan laifukan kisan kai da fashi da makami.

Babban Kwamandan Runduna ta 82, Manjo-Janar Oluyemi Olatoye, ne ya kaddamar da kotun sojin a ranar 18 ga Fabrairu, 2025, domin yanke hukunci kan shari’o’in da suka shafi ma’aikatan da suka yi kuskure a cikin Rundunar.

A cewarsa, waɗannan hukunce-hukuncen sai sun samu tabbatarwa daga hukumomin soji da suka dace, wanda ya nuna ƙarshen shari’o’in sojojin.

Ya sake jaddada ƙudurin Sojojin Najeriya na tabbatar da ɗa’a da kuma kiyaye mafi girman ƙa’idoji na ɗabi’u da ƙwarewa.

“Kuskuren ayyukan wasu kaɗan ba su nuna ƙimar ƙungiyar ba. A koyaushe ana ɗaukar matakai masu sauri da kuma ƙarfi don tabbatar da riƙon amana da adalci,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114