Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar
Published: 5th, March 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya rage lokutan aiki ga ma’aikatan jihar Jigawa a wannan lokaci na azumin watan Ramadan na shekarar 2025.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Muhammad K. Dagaceri ya sanyawa hannu, aka kuma bai wa gidan rediyon Najeriya a Dutse.
“Ma’aikatan jihar za su je aiki karfe 9 na safe sannan su tashi da karfe 3 na rana daga ranar Litinin zuwa Alhamis maimakon zuwa karfe 5 da ake kai wa a baya, sai ranar Juma’a ma’aikatan za su je aiki da karfe 9 na safe su tashi da karfe 1 na rana kamar yadda aka saba”.
Shugaban ma’aikatan ya bayyana cewa, an yi wannan karimci ne da nufin samarwa ma’aikatan gwamnati damammaki masu yawa na shirye-shiryen hutun watan Ramadan da kuma kara himma wajen gudanar da ayyukan ibada da ke da alaka da wannan wata mai alfarma.
“Ana fatan ma’aikatan gwamnati a jihar za su yi amfani da lokacin watan Ramadan wajen yi wa jiharmu addu’a da neman albarkar Ubangiji,” in ji shugaban ma’aikatan.
Alhaji Muhammad Dagaceri ya kara jaddada bukatar ma’aikatan gwamnati su yi amfani da lokacin azumi wajen yin addu’ar zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin jihar da ma Najeriya baki daya.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki
Likitoci a jihar Lagos na tarayyar Najeriya sun fara yajin aiki na gargadi na kuma kwanaki 3 saboda nuna rashin amincewasu da rage hakkokinsu da kuma hanasu kudadensu wanda gwamnatin jihar take yi.
Jaridar Premium times ta Najeriya ta bayyana cewa duk tare da kokarin da ma’aikatar kiwon lafiya ta yi don kada likitocin su shiga yajin aiki amma a safiyar jiya litinin likitocin sun dakatar da ayyuka a dukkan asbitocin gwamnatin Jihar.
A bangaren kasha na jami’ar koyon aikin likita na Jami’ar Lagos marasa lafiya da dama sun fito don ganin likotocinsu amma sai aka fada masu duk sun shiga ya jin aiki. Wanta marasa lafiya wacce taki fadar sunanta ta fadawa Premium times kan cewa ta zo ganin likita amma an ce mata sai ranar 4 ga watan Augusta ta dawo. Kuma kafarta yana mata ciwo sosai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta July 29, 2025 Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba July 29, 2025 Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta July 29, 2025 Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza July 29, 2025 Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine July 29, 2025 Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran July 29, 2025 Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza July 29, 2025 Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba July 28, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci