Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Rage Lokutan Aiki Ga Ma’aikatan Jihar
Published: 5th, March 2025 GMT
Gwamna Umar Namadi ya rage lokutan aiki ga ma’aikatan jihar Jigawa a wannan lokaci na azumin watan Ramadan na shekarar 2025.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban ma’aikata na jihar Alhaji Muhammad K. Dagaceri ya sanyawa hannu, aka kuma bai wa gidan rediyon Najeriya a Dutse.
“Ma’aikatan jihar za su je aiki karfe 9 na safe sannan su tashi da karfe 3 na rana daga ranar Litinin zuwa Alhamis maimakon zuwa karfe 5 da ake kai wa a baya, sai ranar Juma’a ma’aikatan za su je aiki da karfe 9 na safe su tashi da karfe 1 na rana kamar yadda aka saba”.
Shugaban ma’aikatan ya bayyana cewa, an yi wannan karimci ne da nufin samarwa ma’aikatan gwamnati damammaki masu yawa na shirye-shiryen hutun watan Ramadan da kuma kara himma wajen gudanar da ayyukan ibada da ke da alaka da wannan wata mai alfarma.
“Ana fatan ma’aikatan gwamnati a jihar za su yi amfani da lokacin watan Ramadan wajen yi wa jiharmu addu’a da neman albarkar Ubangiji,” in ji shugaban ma’aikatan.
Alhaji Muhammad Dagaceri ya kara jaddada bukatar ma’aikatan gwamnati su yi amfani da lokacin azumi wajen yin addu’ar zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin jihar da ma Najeriya baki daya.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp