Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Published: 1st, March 2025 GMT
‘Fake Inbestment Schemes’: Masu cuta na amfani da shafukan zuba jari na bogi domin damfarar mutane.
Ransomware: Wasu barayin yanar gizo na saka kwayoyin cutar kwamfuta domin su hana mutum amfani da na’urarsa sai ya biya kudi.
Hanyoyin Kare Kanka
Yi amfani da kwayoyin kalmomin sirri masu karfi – A guji amfani da kalmomin sirri kamar sunanka ko shekarunka.
Yi amfani da Two-Factor Authentication (2FA) – Wannan yana 1ara kariya ga asusunka.
Guji danna hadin gwiwa (links) daga tushe da ba a san su ba – Yawancin wadannan hanyoyin suna da cutarwa.
Ka tabbata cewa shafin da kake ziyarta yana da alamar ‘https’ – Wannan yana nuna cewa shafin yana da kariya.
Kar ka raba bayanan sirrinka da kowa – Kar a taba bayar da PIN, OTP, ko wasu muhimman bayanai.
Labari Mai Karfafa Gwiwa
Akwai wata mata mai suna Zainab wacce ta samu sako daga wani wanda ya ce ta ci kyautar N500,000. Da yake tana da ilimi a kan Phishing, ta lura cewa sakon yana da alamun yaudara. Ta guji danna link da aka tura mata kuma ta sanar da abokanta domin su kare kansu. Wannan yana nuna cewa sanin dabarun kare kai a intanet yana da matukar muhimmanci.
Kammalawa
A duniyar intanet, dole ne kowa ya kasance cikin shiri domin guje wa damfarar yanar gizo. Mu kasance masu taka-tsantsan da duk wani bayani da muke rabawa a intanet. Kada mu yarda da komai da muke gani online sai mun tabbatar da gaskiyarsa.
Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
Wannan ya sa wasan yau zai zama mai ɗaukar hankali, domin kowanne daga cikinsu na burin ɗaukar kofin a karo na farko, domin a dakatar da yawan dariyar da ‘yan adawa ke musu.
A zagayen rukuni da suka haɗu a farkon wannan kakar, Arsenal ta lallasa PSG da ci 2-0.
Kocin Arsenal yanzu, Mikel Arteta, ya taɓa buga wasa a duka ƙungiyoyin.
Yana fatan ya zama kocin farko da zai jagoranci Arsenal ta lashe kofin Zakarun Turai.
Wannan ya sa magoya bayan Arsenal ke fatan ganin ƙungiyarsu ta yi abin mamaki a wasan da za a fara da misalin ƙarfe 8 na dare agogon Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp