Aminiya:
2025-05-28@14:53:43 GMT

Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta

Published: 1st, March 2025 GMT

Azumin watan Ramadan na daga cikin shika-shikan Musulunci, kuma Allah ne Ya wajabta shi a kan bayinsa.

Wannan wata yana da falala da lada mai yawa, domin Allah Ya keɓe shi da girma da ɗaukaka.

Ga wasu daga cikin falalar azumin watan Ramadan:

1. Ana buɗe kofofin Aljanna, ana rufe ƙofofin wuta, kuma ana ɗaure shaiɗanu.

Wannan yana taimaka wa zuciyar Musulmi wajen yin alheri da kauce wa munanan ayyuka.

2. Yin azumi da tsayuwar sallar Tarawihi saboda Allah da neman lada, ana gafarta zunuban bawa da suka gabata.

3. Akwai daren Lailatul-Kadari, wanda ya fi wata dubu daraja. Duk wanda ya yi ibada a wannan dare yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa na baya.

4. Yin Umara a watan Ramadan yana daidai da yin aikin Hajji tare da Manzon Allah (SAW).

5. Watan Ramadan wata ne na Alƙur’ani, saboda a cikinsa aka saukar da shi. Don haka, ya dace a yawaita karanta shi.

6. Watan Ramadan wata ne na kyauta, ciyarwa da sadaka. Manzon Allah (SAW) ya fi yawan kyauta a wannan wata.

7. Baccin mai azumi ibada ne, domin yana rage sha’awa da kula da zuciya.

8. Mai azumi yana da farin ciki biyu:

Yayin da zai buɗe baki bayan azumi. Lokacin da zai haɗu da Allah (S.W.A.) ranar alƙiyama.

9. Azumi garkuwa ne daga wutar Jahannama. Yana kare mutum daga sharrin sha’awa da zunubi.

10. A Ramadan, Allah Yana ’yantar da bayinsa daga wuta. Duk wani dare, Allah Yana yafe wa bayinsa kuma yana kuɓutar da su daga azabar lahira.

Wannan wata mai albarka yana ƙarfafa imani, ibada, da kyautatawa.

Don haka, ya kamata Musulmi su yi amfani da watan Ramadan don samun kusanci ga Allah da aikata kyawawan ayyuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kyautatawa Manzon Allah SAW Ramadan watan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Mummunan Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 19 A Kogi

Wani haɗarin mota da ya faru a yau Lahadi a hanyar Lokoja-Obajana ya yi sanadiyar mutuwar mutane 19, yayin da wasu 8 suka jikkata.

Sakataren FRSC na jihar, Kumar Tsukwam, ya tabbatar da cewa haɗarin ya faru ne sakamakon gudun da ya wuce ƙima. Mota bas da wata babbar mota sun yi karo da juna a Gada biyu, inda yara 5 suka ƙone har lahira.

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 2 A Kano – FRSC  Kashi 25 Kawai Na Motocin Da Ke Nijeriya Suke Da Inshora – FRSC

Mutane 27 ne haɗarin haɗarin ya rutsa da su, 8 kacal suka tsira,” in ji Tsukwam. An kai wadanda suka tsira asibitin Fisayo a Obajana don samun kulawa.

FRSC ta yi kira ga direbobi su guje wa gudu da ya wuce gona da iri.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji
  • ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano
  • Ko Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Trump Ya Gujewa Yaki Da Yemen Har Ya Kai Ga Fusata Kawayen Amurka
  • An ga watan Babbar Sallah a Saudiyya
  • Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a Abuja
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 19 A Kogi
  • Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana
  • Kasar Uganda Ta Yanke Huldar Husoje Da Kasar Jamus Bayan Sabanin Diblomasiyya A Tsakaninsu
  • Sheikh Na’im Kassim: Gwagwarmaya Tana Da Wata Hanyar Ta Korar ‘Yan Mamaya