Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta
Published: 1st, March 2025 GMT
Azumin watan Ramadan na daga cikin shika-shikan Musulunci, kuma Allah ne Ya wajabta shi a kan bayinsa.
Wannan wata yana da falala da lada mai yawa, domin Allah Ya keɓe shi da girma da ɗaukaka.
Ga wasu daga cikin falalar azumin watan Ramadan:
1. Ana buɗe kofofin Aljanna, ana rufe ƙofofin wuta, kuma ana ɗaure shaiɗanu.
2. Yin azumi da tsayuwar sallar Tarawihi saboda Allah da neman lada, ana gafarta zunuban bawa da suka gabata.
3. Akwai daren Lailatul-Kadari, wanda ya fi wata dubu daraja. Duk wanda ya yi ibada a wannan dare yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa na baya.
4. Yin Umara a watan Ramadan yana daidai da yin aikin Hajji tare da Manzon Allah (SAW).
5. Watan Ramadan wata ne na Alƙur’ani, saboda a cikinsa aka saukar da shi. Don haka, ya dace a yawaita karanta shi.
6. Watan Ramadan wata ne na kyauta, ciyarwa da sadaka. Manzon Allah (SAW) ya fi yawan kyauta a wannan wata.
7. Baccin mai azumi ibada ne, domin yana rage sha’awa da kula da zuciya.
8. Mai azumi yana da farin ciki biyu:
Yayin da zai buɗe baki bayan azumi. Lokacin da zai haɗu da Allah (S.W.A.) ranar alƙiyama.9. Azumi garkuwa ne daga wutar Jahannama. Yana kare mutum daga sharrin sha’awa da zunubi.
10. A Ramadan, Allah Yana ’yantar da bayinsa daga wuta. Duk wani dare, Allah Yana yafe wa bayinsa kuma yana kuɓutar da su daga azabar lahira.
Wannan wata mai albarka yana ƙarfafa imani, ibada, da kyautatawa.
Don haka, ya kamata Musulmi su yi amfani da watan Ramadan don samun kusanci ga Allah da aikata kyawawan ayyuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kyautatawa Manzon Allah SAW Ramadan watan Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.
A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar DukkuDarekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.
DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.
Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.
Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.