Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Nemi Hadin Kan Al’ummar Jihar Jigawa
Published: 26th, February 2025 GMT
Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa ta bukaci hadin kan al’ummar jihar domin samun nasarar ayyukan da ta sanya a gaba.
Shugaban Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) Barista Salisu Abdu ya bayyana a matsayin wani muhimmin mataki na ci gaba da kokarin tabbatar da gaskiya da rikon amana a bangaren gwamnati.
Ya furta haka ne a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa ta shirya a cibiyar bunkasa ma’aikata dake Dutse.
Ya jaddada cewa, gaskiya, da rikon amana, su ne ginshikin gudanar da shugabanci nagari.
Barista Salisu Abdu, ya kuma yi kira da a hada kai tsakanin Hukumar da hukumomin gwamnati domin yakar cin hanci da rashawa yadda ya kamata.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, taron ya hada manyan masu ruwa da tsaki, da suka hada da wakilai daga ma’aikatar shari’a, shari’a, da ICPC, da EFCC, da PCC, inda aka mayar da hankali wajen ilmantar da mahalarta taron game da aikin hukumar, da tsarin shari’a, da kuma bangarorin hadin gwiwa.
Tattaunawar ta ta’allaka ne kan ingantattun ayyuka, da hanyoyin hana almundahana da ayyukan rashawa.
Taron bitar wanda ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ma’aikatan gwamnati, da masu ruwa da tsaki, ya yi nuni da yadda gwamnati mai ci ke kokarin inganta shugabanci nagari da kawar da cin hanci da rashawa domin share fagen samun ci gaba mai ma’ana a jihar.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cin Hanci Da Rashawa Jigawa da rashawa ta
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
Haka kuma ya nemi kotu da ta bayar da umarnin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kuɗi na Naira 200, 500 da kuma 1000.
Baya ga haka, ya buƙaci a umarci su da su nemi gafara ta hanyar wallafa bayani a manyan jaridu biyu na ƙasa.
Amma a zaman kotu na ranar Litinin, wanda ya shigar da ƙarar da lauyansa ba su halarci zaman kotu ba.
Lauyan da ke kare Emefiele da CBN, Mista Chikelue Amasiani, ya sanar da kotu cewa tun da aka shigar da ƙarar, mai ƙarar da lauyansa ba su nuna wata alama ta son ci gaba da shari’ar ba.
Ya roƙi kotun da ta kori ƙarar.
Mai shari’a Ekwo ya amince da buƙatar kuma ya kori ƙarar, inda ya bayyana cewa mai ƙarar zai iya dawo da ita idan ya shirya yin shari’ar da gaske.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp