Hukumar JSPCACC Ta Kwato Kudaden Gwamnati Sama Da Naira Miliyan 300
Published: 25th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta nemi hadin kan al’umma don gina kasa bisa gaskiya da rikon amana, tare da kaucewa cin hanci da rashawa ba.
Gwamna Umar Namadi ya yi wannan kiran a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) ta shirya a Dutse.
Malam Umar Namadi ya bayyana cewa, taron na da nufin wayar da kan manyan jami’an gwamnati kan ayyukan hukumar da sauran batutuwan da suka shafi hakan.
“Wannan shiri yana da matukar muhimmanci idan aka yi la’akari da yadda gwamnati ta jajirce wajen ci gaba da inganta dukkan ka’idojin gudanar da mulki.”
Gwamna Namadi ya ce, cin hanci da rashawa al’ada ce da ta yadu da ke wargaza al’umma, da cibiyoyin gwamnati.
Ya yi nuni da cewa, shugabanci nagari wanda ya hada da kaucewa rikon sakainar kashi da kin bin son zuciya, sgi ne hanya daya tilo ta yaki da talauci, da ci gaban al’umma cikin sauri, da samar da sauye-sauye masu kyau a cikin al’umma.
Ya ce, ingantaccen tsarin mulki, wanda ke tattare da rikon amana da gaskiya, shi ne tabbacin samun nasara a yakin da ake da talauci, da saurin ci gaban tattalin arziki, da sauye-sauye a tsakanin al’umma.
Namadi wanda ya bayyana gagarumin ci gaban da hukumar ta samu tun bayan kafa ta a shekarar 2022, ya bayyana cewa, ta kwato sama da naira miliyan 300 na kudaden gwamnati, tare da warware kusan rabin korafe-korafe 200 da aka samu, kuma a halin yanzu ta gurfanar da wasu kararraki 16.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Matakin hana malaman da ba su da rajista hawa mumbari a Neja yana ci gaba da yamutsa hazo a ciki da wajen jihar.
Yayin da wasu suke ganin wannan mataki bai dace ba, wasu kuwa gani suke faduwa ta zo daidai da zama, wato matakin ya zo a daidai lokacin da ake bukata.
NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau UkuShirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kan tanadin Dokar Kasa game da wannan batu.
Domin sauke shirin, latsa nan