Gwamnatin jihar Jigawa ta nemi  hadin kan al’umma don gina kasa bisa gaskiya da rikon amana, tare da kaucewa cin hanci da rashawa ba.

Gwamna Umar Namadi ya yi wannan kiran a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) ta shirya a Dutse.

Malam Umar Namadi ya bayyana cewa, taron na da nufin wayar da kan manyan jami’an gwamnati kan ayyukan hukumar da sauran batutuwan da suka shafi hakan.

“Wannan shiri yana da matukar muhimmanci idan aka yi la’akari da yadda gwamnati ta jajirce wajen ci gaba da inganta dukkan ka’idojin gudanar da mulki.”

Gwamna Namadi ya ce, cin hanci da rashawa al’ada ce da ta yadu da ke wargaza al’umma, da cibiyoyin gwamnati.

Ya yi nuni da cewa, shugabanci nagari wanda ya hada da kaucewa rikon sakainar kashi da kin bin son zuciya, sgi ne hanya daya tilo ta yaki da talauci, da ci gaban al’umma cikin sauri, da samar da sauye-sauye masu kyau a cikin al’umma.

Ya ce, ingantaccen tsarin mulki, wanda ke tattare da rikon amana da gaskiya, shi ne tabbacin samun nasara a yakin da ake da talauci, da saurin ci gaban tattalin arziki, da sauye-sauye a tsakanin al’umma.

Namadi wanda ya bayyana gagarumin ci gaban da hukumar ta samu tun bayan kafa ta a shekarar 2022, ya bayyana cewa, ta kwato sama da naira miliyan 300 na kudaden gwamnati, tare da warware kusan rabin korafe-korafe 200 da aka samu, kuma a halin yanzu ta gurfanar da wasu kararraki 16.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya

Uwargidan Shugaban Nijeriya, Sanata Remi Tinubu ta bayar da tallafin naira biliyan daya ga wadanda harin nan ya rutsa da su a yankin Yelwata na Ƙaramar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.

Sanata Tinubu wadda ta miƙa cakin kuɗin ga Gwamna Hyacinth Alia ta sanar da bayar da tallafin ne a jawabinta na jaje wanda ta kai Fadar Gwamnatin Benuwe da ke Makurdi.

Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China

Uwargidan shugaban ƙasar ta buƙaci a yi amfani da wannan tallafin a matsayin gudunmawar farfaɗo da yankin da waɗanda suka tsallake rijiya da baya a yayin harin musamman yaran da yanzu ke buƙatar komawa makarantu.

Ana iya tuna cewa, tun a daren ranar 13 ga watan Yuni zuwa wayewar gari 14 ga watan ne aka kashe fiye da mutum 100 a ƙauyen Yelwata, lamarin da ya janyo Allah wadai daga sassa daban-daban a faɗin ƙasar.

Jihar Benuwe dai na daga cikin jihohin da ke fuskantar matsalar tsaro a Nijeriya, musamman rikicin manoma da makiyaya da kuma na ƙabilanci, wanda ke sanadiyyar salwantar rayuka da dama.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata