Hukumar JSPCACC Ta Kwato Kudaden Gwamnati Sama Da Naira Miliyan 300
Published: 25th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Jigawa ta nemi hadin kan al’umma don gina kasa bisa gaskiya da rikon amana, tare da kaucewa cin hanci da rashawa ba.
Gwamna Umar Namadi ya yi wannan kiran a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) ta shirya a Dutse.
Malam Umar Namadi ya bayyana cewa, taron na da nufin wayar da kan manyan jami’an gwamnati kan ayyukan hukumar da sauran batutuwan da suka shafi hakan.
“Wannan shiri yana da matukar muhimmanci idan aka yi la’akari da yadda gwamnati ta jajirce wajen ci gaba da inganta dukkan ka’idojin gudanar da mulki.”
Gwamna Namadi ya ce, cin hanci da rashawa al’ada ce da ta yadu da ke wargaza al’umma, da cibiyoyin gwamnati.
Ya yi nuni da cewa, shugabanci nagari wanda ya hada da kaucewa rikon sakainar kashi da kin bin son zuciya, sgi ne hanya daya tilo ta yaki da talauci, da ci gaban al’umma cikin sauri, da samar da sauye-sauye masu kyau a cikin al’umma.
Ya ce, ingantaccen tsarin mulki, wanda ke tattare da rikon amana da gaskiya, shi ne tabbacin samun nasara a yakin da ake da talauci, da saurin ci gaban tattalin arziki, da sauye-sauye a tsakanin al’umma.
Namadi wanda ya bayyana gagarumin ci gaban da hukumar ta samu tun bayan kafa ta a shekarar 2022, ya bayyana cewa, ta kwato sama da naira miliyan 300 na kudaden gwamnati, tare da warware kusan rabin korafe-korafe 200 da aka samu, kuma a halin yanzu ta gurfanar da wasu kararraki 16.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
Wani wanda ake zargi da safarar sassan jikin ɗan Adam ya shaida wa jami’an tsaro cewa ya shafe sama da shekara 10 yana sayar da sassan jikin mutum don samun kuɗi.
Dubun mutumin sun cika ne a ranar Asabar din da ta gabata inda sojoji suka kama shi a yankin Kulanla Odomoola da ke Jihar Ogun.
A furucinsa da ya amsa laifin, wanda ake zargin ya amince da sayar da sassan jikin mutum ga masu buƙata don samun kuɗin shiga.
“Na dogara ne da sayar da sassan jikin mutum tsawon shekaru 10 da suka gabata. Yawancin sassan da nake sayarwa ina tono su ne daga sabbin kaburbura a makabartu, yayin da wasu kuma nake samun su daga gawarwakin da aka watsar a gefen hanyoyi,” in ji shi.
Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”Wanda ake zargin, wanda ya amsa laifinsa ga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi kafin sojoji su cece shi, ana zargin yana kan hanyarsa ne na kai wani sassan jiki ga wani mai siye lokacin da aka kama shi.
Daga nan aka miƙa wanda ake zargin ga ’yan sanda a yankin Noforija don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.
Laftanar Kanar Olabisi Olalekan Ayeni, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Sojin Najeriya ta 81, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayan kama wanda ake zargin daga baya an miƙa shi tare da kayayyakin da aka samu a wurinsa, ga ’yan sandan Najeriya don ƙarin bincike da kuma gurfanar da shi a gaban kotu.
“Sojojin sun ceto wanda ake zargin daga wani taron jama’a da suka yi yunƙurin kashe shi,” in ji shi.