Magidanci ya sari matarsa da adda har lahira
Published: 25th, February 2025 GMT
’Yan sanda sun cika hannu da wani magidanci bayan da ya sari matarsa da adda a kai, ta ce ga garinku nan.
’Yan sanda sun kama magidancin ne bayan samun rahoton aika-aikan da ya yi wa mai dakin tasa a sakamakon takaddamar da suka samu a tsakaninsu.
Lamarin ya faru ne a sabuwar unguwar Upper Mission da ke garin Benin, hedikwatar Jihar Edo.
Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce ko da ’yan sanda daga babban ofishinsu da ke yankin Aduwawa suka isa wurin, sun iske matar kwance cikin jini, da mummunan sara a kanta.
Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700 NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’aYa ce, al’ummar yankin sun nemi su halaka shi saboda saran matar tasa da ya yi da makami, amma ya sha da kyar.
Ya bayyana cewa da kyar ’yan sanda suka kwaci mutumin daga hannun jama’a, suka tafi da shi domin tsarewa da kuma yi masa tambayoyi.
CSP Moses Yamu ya ce ’yan sanda sun kai matar asibiti inda likita ya shaida musu cewa rai ya riga ya yi halinsa.
Jami’in ya kara da cewa Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Edo, Betty Otimenyin, ya koka bisa yadda ake samu karuwar fada da makami a tsakanin ma’aurata a jihar.
Daga nan ya ba da umarnin a gudanar da zuzzurfan bincike kan lamarin domin hukunta mai laifi yadda doka ta tanadar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
Wata mummunar guguwa ta yi sanadin mutuwar mutum shida sannan ta jikkata wasu 30 a garin Garba-Chede da ke karamar hukumar Bali a jihar Taraba.
A cewar wani mazaunin yankin wanda guguwar ta lalata wa gida mai suna Abubakar Dodo, an shafe shekaru masu yawa ba su ga irin ta ba a yankin saboda munin barnar da ta yi.
Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a FilatoA cewarsa, ban da gidaje, guguwar ta kuma lalata makarantu da masallatai da coci-coci, sannan kayan abinci na miliyoyin Naira sun salwanta.
Dagacin garin na Garba-Chede, Kaigama Maigandi, ya yi kira ga Gwamnan Jihar, Agbu Kefas, da ya taimaka wa mutanen yankin da iftila’in ya shafa domin su samu su gyara gidaje da wuraren kasuwancinsu.
A wani labarin kuma, wata tawagar wakilai daga Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), ta ziyarci yankin domin jajanta musu da kuma ganin girman barnar domin ganin irin tallafin da za a yi musu.
Ayarin, wanda ke karkashin jagorancin Dr. Balutu Isa Mohammed, ya yi jaje ga mutanen tare da yi musu alkawarin ba su tallafin muhimman abubuwan da suke bukata domin su rage radadi.
Tawagar ta kuma ziyarci Dagacin garin tare da yi masa bayanin musabbabin zuwansu da kuma ayyukan da suke yi.