Aminiya:
2025-06-13@10:50:01 GMT

Uwa ta jefo jaririnta daga saman bene mai hawa biyu

Published: 24th, February 2025 GMT

Wani jariri sabuwar haihuwa ya riga mu gidan safiyar Litinin bayan mahaifiyarsa ta jefo shi ta tagar wani otel a birnin Paris. Jami’an tsaro da ke shigar da ƙara sun ce an tsinci gawar jaririn wanda ko cibiyarsa ba a yanke ba. An yi zanga-zangar kisan ɗalibi a Jami’ar FUDMA da ke Katsina NNPP ta dakatar da Kawu Sumaila da Ali Madakin Gini Wata majiya ta ce uwar jaririn mai shekaru 18 ta jefo shi ne ta tagar ɗakin wani otel daga hawa na biyu a Kudancin Faransa.

An bai wa jaririn kulawar gaggawa amma a ƙarshe ya ce ga garinku nan kamar yadda majiyar ta tabbatar. ’Yan sanda sun ce jaririn ya mutu da misalin ƙarfe 7:45 na safiya agogon GMT a Asibitin Debre kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito.Bayanai sun ce uwar jaririn wadda ɗaliba ce ’yar asalin ƙasar Amurka ta jefo jaririn ne bayan haihuwarsa a ɗakin da ke hawa na biyu na otel ɗin

Tuni dai mahukunta a Faransa suka ƙaddamar da bincike kan lamarin yayin da suka tabbatar da cafke matashiyar da ake zargi.

An ruwaito cewa BaAmurkiyar na daga cikin tawagar wasu matasan ɗalibai da ke yawon ƙaro ilimi a nahiyar Turai.

A halin yanzu dai an kai matashiyar asibiti domin samun kulawar da ta dace a sanadiyar haihuwar da ta yi a yayin da bincike zai ci gaba da gudana.

 

AFP

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jariri Paris Uwa

এছাড়াও পড়ুন:

An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari

Babban baturen ’yan sanda na birnin Ahmedabad da ke ƙasar Indiya ya bayyana cewa, an ciro gawar mutane sama da 200 na fasinjojin jirgin Air India da ya yi hatsari a yau Alhamis.

Babban jami’in ɗan sandan ya bayyana hakan ne a matsayin bayani na baya-bayan nan kan hatsarin jirgin, wanda ya rikito ƙasa jim kadan bayan tashi, kan hanyarsa ta zuwa birnin London na Birtaniya.

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya

Shugaban hukumar kula da sufurin jiragen sama na Indiya ya ce jirgin na ɗauke ne da mutum 242, kuma akasarinsu Indiyawa ne.

Fasinjojin jirgin Indiya da yawa sun mutu a hatsarin

A cewar Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ambato shugaban ƴan sanda na birnin Ahmedabad na cewa akwai yiwuwar babu wanda ya tsira da ransa a hatsarin da jirgin sama mallakin kamfanin sufuri na India Air ya faru yau a birnin.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake bayani kan hatsarin jirgin da ke kan hanyarsa ta zuwa birnin London na ƙasar Birtaniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
  • Tawagar Fursininin Yaki Na Rasha Sunn Koma Gida Daga Kieve
  • Isra’ila ta sake kashe Falasdinawa a wurin rabon tallafi
  • Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A Kano