Yadda jama’a suka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga
Published: 24th, February 2025 GMT
Al’ummar gari sun wani ɗan shekara 65 dauke da bindiga sun damƙa shi a hannun hukumar ’yan sanda.
Rundunar ’yan sandan Jihar Akwai Ibom ta kama mutumin ne tare da wani abokinsa da bindiga kirar ‘Double Barrell’ da harsasai da cocila da sauran kayayyaki a cikin wata kakar matafiya.
Kakakin rundunar, DSP Timfon John, ya ce dubun dan shekara 65 din mai suna Nehemiah Sunday Udo ne a ranar Asabar baya al’ummar kauyen Ekpene Obo da ke Ƙaramar Hukumar Esit Eket sun ritsa shi.
John ya ce bayan samun kira daga al’ummar yankin ne ’yan sanda suka kai samame inda suka samu mutanen sun kai wanda ake zargin fadar basaraken yankin.
Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi kan shan mangwaro a makaranta NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar BiriYa ce ’yan sanda sun je fadar inda a suka yi awon gaba da wanda ake zargin zuwa hedikwatarsu ta jihar, kuma Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Baba Mohammed Azare, ya sa a gudanar da bincike kan lamarin.
Ya ce a yayin bincike “wanda ake zargin ya yi ikirarin cewa shi mamba ne a kungiyar kwararrun maharba, amma ana ci gaba da bincike domin gano gaskiyar da kuma haƙiƙanin manufarsa, in ji John.
Jami’in ya kara da cewa mutum na biyun kuma ’yan sanda ne suka kama shi ɗauke da karamar bindigar hannu a wani shigen bincike a kan hanyar Ikot Udoma da ke yankin Eket.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda shekara 65
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae, a karon farko da yayi magana dangane da fashewar tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae ya gabatar da Ta’ziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu ko suka jikata a wannan hatsarin. Ya kuma bukaci a gudanar da bincike mai mai zurfi don gano musabbabin fashewar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jagoran yana bada umurni ga ma’aikatar shari’aa a kasar ta gudanar da cikekken bincike don sanin abinda ya faru saboda daukar matakan da suka dace don hana irin wannan sake faruwa nan gaba, sannan idan akwai wadanda suka yi kuskure a hukunta su.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gobarar da ta taso a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajae, daya daga cikin tashoshin jirage masu muhimmanci a tattalin arzikin kasar, don haka dole ne a kara daukar matakan tsaro da amincin tashar don hana irin wannan sake faruwa.
Sanadiyyar wannan hatsarin majalisar dokokin kasar ta shelanta makoki a duk fadin kasar a yau Litinin. Sannan shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan ya ziyarci tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae don ganewa idanunsa abubuwan da suka faru da kuma barnan da aka tabka.
Ya zuwa yanzun wadanda suka rasa rayukansu sun kai 40 sannan wadanda suka rasa rayukansu sun kai dubu guda.