Aminiya:
2025-11-02@06:24:48 GMT

Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi saboda shan mangwaro a makaranta

Published: 24th, February 2025 GMT

Ana zargin malamin makarantar Aliyu Mustapha Academy da ke Jimeta a Jihar Adamawa kan wuce gona da iri da kuma azabtar da wani ɗalibinsa a dalilin shan mangwaro a lokacin ‘break’ a harabar makarantar.

Aminiya ta ruwaito cewa a lokacin da ake tsaka da hutun tara ne malamin yan kama ɗalibin yana shan mangwaro, inda ya lakaɗa wa ɗalibin dukan tsiya.

Shaidu sun ce har da naushi malamin ya riƙa yi wa ɗalibin, lamarin da ya sa taron ya ƙuƙƙuje tare da barin sa da tabbai a jikinsa.

Malamin yana tsaka da dukan ɗalibin ne mahaifin yaron ya je makarantar domin tabbatar da biyan kudin makarantar ɗan nasa.

NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi

Ganin halin da ya iske ɗan nasa a sai ya sanya baki, amma malamin bai dakata ba da naushin yaron.

Mahaifin mai suna Bashiru Haman, ya ce, “Na kaɗu da ganin ana dukan yaron haka, na yi ƙoƙarin in ƙwace shi amma malamin ya ƙi barin sa. Daga nan sai an kai ƙara wajen shugabar makarantar, Misis Amanda Pam, Amma sai ta umarce ni da in fice daga harabar makarantar.”

Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Adamawa, A’isha Yanar ta tabbatar da faruwar lamarin. Ta ce, “ma’aikatar ta samu wasikar ƙorafin mahaifin ɗalibin kuma ta fara gudanar da bincike domin daukar matakin da ya dace. Za kuma mu ɗauki matakan da suka kamata domin hana faruwar irin haka a nan gaba.”

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Adamawa ta ce ta fara gudanar da bincike kan lamarin, kamar yadda kakakinta, Dankombo Morris, ya sanar.

Ya ce, “muna kira da duk masu wani bayani game da abinda ya faru da su taimaka mana da bayanai a wannan bincike da muke gudanarwa.”

A halin yanzu dai yaron mai suna Jaafar yana fama da jinya a yayin da iyayensa suke neman a ƙwato masa haƙƙi kan azabtarwar da aka yi masa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibi Jihar Adamawa Shan mangwaro

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

A cewar ta a cikin shekarar 2024 jihar Katsina kawai ta samu masu wannan cuta mutum 17 tare da guda biyu a karamar hukumar Danmusa a cikin wannan shekara

Haka kuma Hajiya Zulaihat Radda ya bada tabbacin cewa kowane yaro an tabbatar da ya amshi allurar Riga-kafin shan Inna

Ana jawabin wakilin asusun tallafawa yara na UNICEF na ofishin Kano, Rahama Mohammed Farah ta yabawa kokarin jihar Katsina na dawo da sabon yunkurin kawar cutar shan Inna a Nijeriya baki daya

Ya kuma bayyana cewa asusun kula da kananan yara na UNICEF Yana hadin gwiwa da gwamnatoci da hukumomi da masu ruwa da tsaki a kananan hukumomi domin ganin wajen fadakar da al’umma akan allurar Riga-kafin shan Inna a jihar Katsina.

Shima da yake jawabi shugaban hukumar lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina Dakta Shansudeen Yahaya ya yi alkawarin cigaba da wayar da kan al’umma akan wannan cuta ta shan Inna da sauran cututtuka masu kashe yara a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

Wadanda suka shaida wannan bikin ranar ‘Polio’ ta duniya sun hada da hukumar lafiya ta WHO da kuma masu lalurar cutar shan Inna da wakilan asusun UNICEF da matan shugabannin kananan hukumomi 34 na jihar Katsina

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025 Manyan Labarai Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai October 31, 2025 Manyan Labarai Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher