Mataimakin Shugaban APC Da Mambobi 7,500 Sun Sauya Sheka Zuwa PDP A Bauchi
Published: 23rd, February 2025 GMT
Mataimakin Shugaban jam’iyyar APC a ƙaramar hukumar Dass ta jihar Bauchi, Yunusa Umar, ya jagoranci mambobi fiye da 7,500 zuwa jam’iyyar PDP. Cikin waɗanda suka sauya sheka har da Shugaban Matasa na APC a yankin, Yusuf Inuwa Bora, da Sakatare mai kula da jin daɗin mambobi, Isah Zakaria.
An karɓi waɗannan sabbin ‘yan jam’iyyar ne a hukumance a ranar Lahadi, inda Shugaban PDP na ƙaramar hukumar Dass, Hon.
Ya jaddada cewa manufofi da shirye-shiryen gwamnan tun bayan hawansa mulki a 2019 sun amfanar da al’umma matuƙa. Ya ce suna da yaƙinin cewa PDP ce ke kula da walwalar jama’a, don haka ba su da dalilin ci gaba da zama a APC. Ya kuma tabbatar da cewa sabbin mambobin za su yi aiki tuƙuru don cigaban PDP a jihar.
Shugaban ƙaramar hukumar, Hon. Jibo, ya bayyana wannan sauya sheƙar a matsayin babbar nasara ga PDP, yana mai cewa gwamnatin Bala Mohammed za ta ci gaba da ɗorewa kan hanyoyin cigaban jihar Bauchi. Ya kuma tabbatar wa sabbin mambobin cewa za su samu cikakkiyar damar zama ‘yan PDP ba tare da nuna bambanci ba.
কীওয়ার্ড: ƙaramar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
Rundunar ’yan sandan ƙasar Australia ta kama wata ’yar asalin Najeriya da ke ƙasar Australia, Binta Abubakar bisa zarginta da safarar ɗalibai daga ƙasar Papua New Guinea tare da tilasta musu yin aikin da ba a biya a gonaki a faɗin jihar Ƙueensland da sunan bayar da tallafin karatu.
Binta mai shekara 56, an kama ta ne a ranar Laraba a filin jirgin saman Brisbane a lokacin da ta isa ƙasar Papua New Guinea, inda take zaune.
Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8 Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiKamen nata ya biyo bayan wani bincike na tsawon shekaru biyu da ƙungiyar masu fataucin bil-Adama ta AFP ta yankin Arewa, wacce ta ƙaddamar da bincike kan ayyukanta a watan Yulin 2022 bayan samun bayanai daga ’yan sandan Ƙueensland.
A cewar AFP, “Wani gungun ‘yan asalin Papua New Guinea (PNG) da suka yi ƙaura zuwa Australia don yin karatu, an yi zargin cewa an tilasta musu yin aiki ba tare da son ransu ba a gonaki.”
An ba da rahoton cewa matar mai izinin zama ƙasashen biyu ta yaudari aƙalla ƴan ƙasar PNG 15, masu shekaru tsakanin 19 zuwa 35, zuwa Australia tsakanin Maris 2021 da Yuli 2023 ta hanyar kamfaninta, BIN Educational Serɓices and Consulting, da kuma ta hanyar ba da guraben karatu na bogi.
Rahoton ya bayyana cewa, shafin intanet na kamfaninta ya yi iƙirarin bayar da “daidaitaccen tsarin zamani don ilimi, horarwa da kuma aikin yi.”
Sai dai ’yan sandan sun ce gaskiyar lamarin ya sha bamban sosai.
Da zarar sun isa Australia, an yi zargin cewa an tilasta wa ɗaliban su sanya hannu kan jerin takaddun doka da ke tilasta su su biya kuɗin da ke da alaƙa da karatun, kuɗin jirgi, aikace-aikacen samar da biza, inshora da kuma kuɗaɗen doka.”