Mataimakin Shugaban APC Da Mambobi 7,500 Sun Sauya Sheka Zuwa PDP A Bauchi
Published: 23rd, February 2025 GMT
Mataimakin Shugaban jam’iyyar APC a ƙaramar hukumar Dass ta jihar Bauchi, Yunusa Umar, ya jagoranci mambobi fiye da 7,500 zuwa jam’iyyar PDP. Cikin waɗanda suka sauya sheka har da Shugaban Matasa na APC a yankin, Yusuf Inuwa Bora, da Sakatare mai kula da jin daɗin mambobi, Isah Zakaria.
An karɓi waɗannan sabbin ‘yan jam’iyyar ne a hukumance a ranar Lahadi, inda Shugaban PDP na ƙaramar hukumar Dass, Hon.
Ya jaddada cewa manufofi da shirye-shiryen gwamnan tun bayan hawansa mulki a 2019 sun amfanar da al’umma matuƙa. Ya ce suna da yaƙinin cewa PDP ce ke kula da walwalar jama’a, don haka ba su da dalilin ci gaba da zama a APC. Ya kuma tabbatar da cewa sabbin mambobin za su yi aiki tuƙuru don cigaban PDP a jihar.
Shugaban ƙaramar hukumar, Hon. Jibo, ya bayyana wannan sauya sheƙar a matsayin babbar nasara ga PDP, yana mai cewa gwamnatin Bala Mohammed za ta ci gaba da ɗorewa kan hanyoyin cigaban jihar Bauchi. Ya kuma tabbatar wa sabbin mambobin cewa za su samu cikakkiyar damar zama ‘yan PDP ba tare da nuna bambanci ba.
কীওয়ার্ড: ƙaramar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
A nata bangare kuwa, Amurka ta bayyana aniyarta ta aiki tare da bangaren Sin, wajen ci gaba da warware sabani a fannonin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar tsarin gudanar da shawarwari, da ingiza damar samar da karin nasarori daga tattaunawar, da kara samar da daidaito a alakar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Sin.
Wakilin cinikayya na kasa da kasa na Sin karkashin ma’aikatar cinikayya, kuma mataimakin ministan cinikayyar kasar Li Chenggang, ya bayyana a yayin da yake yiwa manema labarai karin haske game da zaman tattaunawar sassan biyu. Ya ce sassan biyu suna sane da muhimmancin wanzar da daidaito, da kyautata alakar tattalin arziki mai nagarta tsakanin Sin da Amurka, sun kuma yi kyakkyawar musaya game da muhimman batutuwan cinikayya da na raya tattalin arziki dake jan hakulansu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp