Aminiya:
2025-08-01@10:43:58 GMT

’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci

Published: 23rd, February 2025 GMT

’Yan bindiga sun kai hari wata coci da ke yankin Ogwashi-Uku a Jihar Delta, inda suka yi awon gaba da masu ibada a daren ranar Juma’a.

Sun harbi fasto sannan suka sace masu i ada shida a cocin, lamarin da ya jefa al’umma cikin firgici.

Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba

Sun kai harin ne da misalin ƙarfe 10 na dare kusa da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Delta.

Maharan sun harbi fasto, Apostle Divine Omodia, wanda yanzu haka yake kwance a asibiti.

Mutanen yankin suna cikin fargaba kan rashin tsaro a wuraren ibada, inda suke roƙon gwamnati ta ceto mutanen da aka sace tare da kama waɗanda suka kai harin.

Matar faston, Fasto Faith Omodia, ta bayyana jimaminta kan faruwar lamarin.

Ta ce ’yan bindigar sun buɗe wuta a cikin cocin.

“Na kwanta da jaririna a cikin coci sai na ji harbe-harbe. Kafin na ankara, harsasai sun fara shigowa cikin ɗakin da muke ciki.

“Ɗaya daga cikinsu ya harbe ni, amma harsashin bai shiga jikina ba. Sai dai kawai na ga wuta,” in ji ta.

Ta kuma ce an harbi mijinta a ƙafarsa, sannan ya rasa yatsu biyu.

Bayan haka, ’yan bindigar sun tattara masu ibada, tare da yin awon gaba da mutum shida, ciki har da masu gadin cocin biyu.

Mutanen da aka sace sun haɗa da Helen Onwuamaeze, Ariyo Emmanuel, Chike Okolo, da Blessing Waye, tare da masu gadi biyu da ba a bayyana sunayensu ba.

Rundunar ’yan sandan Jihar Delta ba ta tabbatar da faruwar harin ba tukuna.

Lokacin da aka tambayi kakakin rundunar, Bright Edafe, ya ce babu wani rahoto da aka kai ofishin ’yan sanda kan harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindi6 harbi Jihar delta Mabiya Rauni

এছাড়াও পড়ুন:

Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina

Sama da mutum 5,000 ne suka tsere daga gidajensu a Jihar Katsina, sakamakon sabbin hare-haren da ’yan bindiga suka kai a Ƙananan Hukumomin Bakori da Faskari.

Mutane daga ƙauyuka sama da 10 sun nemi mafaka a garin Bakori, inda da dama ke zaune wajen ’yan uwansu, yayin da wasu ke kwana a waje ba tare da masauki ko abinci ba.

Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura

Wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa sun bayyana cewa, maharan sukan shiga ƙauyuka da yawa, inda suka dinga harbi, ƙone gidaje, sannan suka sace mutane ciki har da mata da ƙananan yara.

Hare-haren sun fi muni a auyuka irin su Guga, Anguwar Danmarka, Gidan Sule, da sauransu.

Wani dattijo mai shekara’u 68 daga ƙauyen Doma ya ce sama da mutum 250 aka kashe a yankinsa cikin shekaru biyar da suka wuce.

Ya ƙara da cewa ’yan bindigar sukan ƙone rumbunan abinci tare da sace dabbobi.

Wata mata da ta kuɓuta daga harin a Anguwar Galadima ta ce iyalinta su 17 sun tsere, inda ta ce an sace sama da mutum 20 a ƙauyen nasu.

Wani saurayi daga Anguwar Dan Marka ya bayyana yadda aka harbe shi sau biyu a ƙafa, kuma yanzu yana amfani da sanda wajen yin tafiya.

Wasu da dama har yanzu suna hannun maharan, yayin da suke neman fansar Naira miliyan 1.5 kan kowane mutum ɗaya.

Manoma ma na kuka da halin da suka tsinci kansu sakamakon hare-haren.

A wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, wani manomi daga Ƙaramar Hukumar Sabuwa ya koka da yadda aka lalata gonarsa.

Amma a martanin da suka bayar, shugabannin Ƙaramar Hukumar sun ce an lalata gonakin da ke kusa da manyan tituna ne domin hana ’yan bindiga amfani da su wajen ɓuya da kuma kai wa matafiya hari.

Amma manoman suna kallon wannan a matsayin wata matsala a gare su.

Shugabannin ƙauyuka da hukumomin gwamnati sun tabbatar da cewa mutane suna ƙara zuwa Bakori kowace rana don neman mafaka.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Bakori, ya ce akwai sama da mutum 3,500 da ke zaune a Bakori, yayin da wasu sama da 2,000 ke zaune a ƙauyen Guga.

An fara raba wa waɗanda suka rasa matsugunansu abinci da kayan masarufi, amma ana buƙatar samum ƙarin taimako.

Ƙungiya ta buƙaci a ayyana dokar ta-ɓaci a Bakori

An buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta jiha da kuma ƙungiyoyin agaji su kai wa waɗanda lamarin ya shafa ɗauki cikin gaggawa.

Wata ƙungiya mai zaman kanta mai suna ‘Grassroots Advocates for Peace’ ta nemi Gwamnatin Tarayya ta ayyana Bakori a matsayin yanki mai hatsari.

Sun buƙaci ƙarin jami’an tsaro, da ɗaukar mataki cikin gaggawa.

Sun kuma buƙaci a kula da lafiyar kwakwalwar waɗanda suka kuɓuta daga hare-haren da kuma hukunta masu kai hare-haren.

Gwamnatin Katsina na ƙoƙarin magance matsalar

A nata ɓangaren, Gwamnatin Jihar Katsina, ta ce tana ƙoƙarin wajen magance matsalar.

Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar, Nasir Muazu, ya ce suna ƙoƙarin magance matsalolin da Ƙaramar Hukumar ke fama da su.

Ya ce akwai wasu mutane da ke ƙoƙarin yada ƙarya a kafafen sada zumunta don haifar da tsoro da ruɗani a zukatan jama’a.

Ya kuma ce an samu sauƙin kai hare-hare a wasu yankuna kamar Jibia da Batsari.

Kwamishinan, ya bayyana cewa an kafa rundunar ‘Katsina Community Watch Corps’ domin taimaka wa sojoji, ’yan sanda da ’yan sa-kai wajen shiga dazuka da ke da wuyar shiga.

Sai dai ya buƙaci jama’a da su ci gaba da jajircewa da kuma bayar da rahoton duk wani abu da su yarda da shi ba.

An samu sauƙin kai hare-hare cikin shekara 2 — Ribadu

A yayin da gwamnati ke cewa ana samun ci gaba, Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkar Tsaro, Nuhu Ribadu, ya ce Najeriya ta fi samun zaman lafiya a yanzu sama da shekaru biyu da suka wuce.

Ya ce an ceto da mutum sama da 11,000 da aka sace, kuma an kashe wasu daga cikin manyan shugabannin ’yan bindiga.

Ya yaba wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, bisa jagoranci da tsare-tsaren tsaro da suka haifar da wannan sauyi.

Sai dai waɗanda ke zaune a matsuguni na wucin gadi a Bakori da wasu yankuna, rayuwa cikin tsaka mai wuya.

Wasu sun ce har yanzu ba su da ƙwarin gwiwar komawa gidajensu.

Sun tabbatar da cewar sai gwamnati ta samar da tsaro mai ɗorewa, sannan za su koma muhallansu, saɓanin haka za su ci gaba da zama a inda suke a yanzu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri