’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci
Published: 23rd, February 2025 GMT
’Yan bindiga sun kai hari wata coci da ke yankin Ogwashi-Uku a Jihar Delta, inda suka yi awon gaba da masu ibada a daren ranar Juma’a.
Sun harbi fasto sannan suka sace masu i ada shida a cocin, lamarin da ya jefa al’umma cikin firgici.
Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — Ata Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zambaSun kai harin ne da misalin ƙarfe 10 na dare kusa da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Delta.
Maharan sun harbi fasto, Apostle Divine Omodia, wanda yanzu haka yake kwance a asibiti.
Mutanen yankin suna cikin fargaba kan rashin tsaro a wuraren ibada, inda suke roƙon gwamnati ta ceto mutanen da aka sace tare da kama waɗanda suka kai harin.
Matar faston, Fasto Faith Omodia, ta bayyana jimaminta kan faruwar lamarin.
Ta ce ’yan bindigar sun buɗe wuta a cikin cocin.
“Na kwanta da jaririna a cikin coci sai na ji harbe-harbe. Kafin na ankara, harsasai sun fara shigowa cikin ɗakin da muke ciki.
“Ɗaya daga cikinsu ya harbe ni, amma harsashin bai shiga jikina ba. Sai dai kawai na ga wuta,” in ji ta.
Ta kuma ce an harbi mijinta a ƙafarsa, sannan ya rasa yatsu biyu.
Bayan haka, ’yan bindigar sun tattara masu ibada, tare da yin awon gaba da mutum shida, ciki har da masu gadin cocin biyu.
Mutanen da aka sace sun haɗa da Helen Onwuamaeze, Ariyo Emmanuel, Chike Okolo, da Blessing Waye, tare da masu gadi biyu da ba a bayyana sunayensu ba.
Rundunar ’yan sandan Jihar Delta ba ta tabbatar da faruwar harin ba tukuna.
Lokacin da aka tambayi kakakin rundunar, Bright Edafe, ya ce babu wani rahoto da aka kai ofishin ’yan sanda kan harin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindi6 harbi Jihar delta Mabiya Rauni
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
Manajar ofishin na NIWA, da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.
Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.
“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.
“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.
Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA, Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa da ke a sassan kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA