Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP
Published: 23rd, February 2025 GMT
Jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa babu wani ɗan Arewa mai mai hankali da zai goyi bayan APC a zaɓen 2027.
PDP ta bayyana hakan ne a matsayin martani kan zargin cewa Sanata Lawal Adamu, Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya, baya aikin komai sai ɗumama kujera.
Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — AtaHaka kuma, ana zargin gwamnatin Jihar Kaduna da dakatar da rarraba kayayyakin koyarwa da Sanata Lawal Adamu ya saya domin amfanin makarantun jihar.
Yusuf Dingyadi, Mataimaki na Musamman na Shugaban PDP kan Yaɗa Labarai, ya ce ya kamata gwamnatin jihar ta haɗa kai da wakilan jama’a don ci gaban al’umma.
“Abin da ake buƙata shi ne gwamnatin jihar, ba tare da la’akari da bambancin siyasa ba, ta haɗa kai da sauran wakilan jama’a don inganta rayuwar al’ummar Kaduna.
“PDP jam’iyya ce mai aƙida, kuma idan har kuna ci gaba da kai mata hari, ba za ku taɓa samun ci gaba ba.
“Ba za ku iya ɗaukar ’yan daba da masu yaɗa farfaganda don ɓata mana suna ba, kawai don ku burge Shugaba Bola Tinubu saboda burinku na 2027.
“Babu wani ɗan Arewa mai hankali da zai yi wa APC kamfe a Arewa.
“Gaskiyar ita ce, wasu ’yan siyasa suna yi masa biyayya ne ba don suna goyon bayansa da gaske ba, sai dai kawai don su samu abinci,” in ji shi.
Dingyadi ya shawarci Gwamna Uba Sani da kada ya bari wasu ’yan siyasa su ruɗe shi.
Ya ƙara da cewa, “’Yan majalisar da PDP ta zaɓa suna aiki tuƙuru. Suna yin ƙoƙari a yankunansu sama da na APC.
“Ba za ku iya daƙile nasarar siyasarmu ta hanyar ɗaukar ’yan farfaganda don su kai wa wakilanmu masu aiki hari ba, ko kuma ta hanyar shirya ficewar ’yan siyasa daga PDP a wuraren da aka shirya da gangan.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa martani Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce sojojin kasar Iran ba za su sararawa gwamnatin Isra’ila ba.
Jagoran ya bayyana hakan ne a wani sakon bidiyo ga al’ummar Iran ranar Juma’a biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta yi kan kasar wanda ya kashe fararen hula, masana kimiyya da kwamandojin soji.
Ayatullah Khamenei ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila ba za ta kubuta daga wannan aika-aika ba, yana mai tabbatar wa al’ummar Iran cewa ba za a yi sakaci kan hakan ba.
Jagoran ya jaddada cewa muguwar gwamnatin sahyoniya ta tafka babban kuskure, sannan kuma shelanta yaki ne kan Iran.
Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa: dukkanin jami’an kasar Iran da bangarori daban-daban na siyasa da kuma al’ummar Iran suna da ra’ayi daya dangane da wajabcin daukar wani mataki mai karfi wajen tunkarar gwamnatin sahyoniya ta ‘yan ta’adda.
Jagoran ya kara da cewa, bai kamata gwamnatin Isra’ila ta yi tunanin cewa ta ci bulus ba, kuma komi ya wuce.