Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP
Published: 23rd, February 2025 GMT
Jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa babu wani ɗan Arewa mai mai hankali da zai goyi bayan APC a zaɓen 2027.
PDP ta bayyana hakan ne a matsayin martani kan zargin cewa Sanata Lawal Adamu, Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya, baya aikin komai sai ɗumama kujera.
Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — AtaHaka kuma, ana zargin gwamnatin Jihar Kaduna da dakatar da rarraba kayayyakin koyarwa da Sanata Lawal Adamu ya saya domin amfanin makarantun jihar.
Yusuf Dingyadi, Mataimaki na Musamman na Shugaban PDP kan Yaɗa Labarai, ya ce ya kamata gwamnatin jihar ta haɗa kai da wakilan jama’a don ci gaban al’umma.
“Abin da ake buƙata shi ne gwamnatin jihar, ba tare da la’akari da bambancin siyasa ba, ta haɗa kai da sauran wakilan jama’a don inganta rayuwar al’ummar Kaduna.
“PDP jam’iyya ce mai aƙida, kuma idan har kuna ci gaba da kai mata hari, ba za ku taɓa samun ci gaba ba.
“Ba za ku iya ɗaukar ’yan daba da masu yaɗa farfaganda don ɓata mana suna ba, kawai don ku burge Shugaba Bola Tinubu saboda burinku na 2027.
“Babu wani ɗan Arewa mai hankali da zai yi wa APC kamfe a Arewa.
“Gaskiyar ita ce, wasu ’yan siyasa suna yi masa biyayya ne ba don suna goyon bayansa da gaske ba, sai dai kawai don su samu abinci,” in ji shi.
Dingyadi ya shawarci Gwamna Uba Sani da kada ya bari wasu ’yan siyasa su ruɗe shi.
Ya ƙara da cewa, “’Yan majalisar da PDP ta zaɓa suna aiki tuƙuru. Suna yin ƙoƙari a yankunansu sama da na APC.
“Ba za ku iya daƙile nasarar siyasarmu ta hanyar ɗaukar ’yan farfaganda don su kai wa wakilanmu masu aiki hari ba, ko kuma ta hanyar shirya ficewar ’yan siyasa daga PDP a wuraren da aka shirya da gangan.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa martani Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
Hukumar Tace Fina-Finai da Dab’i ta Jihar Kano ta haramta shirya duk wata muƙabala tsakanin mawaƙan yabon Annabi (S.A.W), tare da gayyatar mawaƙa Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi su bayyana a gabanta.
Hukumar ta kuma gayyaci mawaƙan ne tare da sauran waɗanda suka jagoranci muƙabalar da fitattun mawaƙan biyu suka yi ranar Litinin, da su bayyana a gabanta cikin sa’o’i 24.
Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin TinubuHakan na zuwa ne ƙasa da kwana ɗaya bayan ɓullar wata muhawara da aka yi tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi kuma ta karade shafukan sada zumunta, wacce hukumar ta bayyana a matsayin karya dokokin aikinta.
Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da hakan ranar Talata, inda ya ce ɗaukar matakin wani yunƙuri ne na tabbatar da zaman lafiya, daidaito da bin doka tsakanin mawaƙan nishaɗi da na addini.
El-Mustapha, a cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar, ya kuma ce an haramta duk wata nau’in muƙabala daga mawaƙan addini a jihar ba tare da izinin hukumar ba.
A yayin da yake ƙaddamar da wani kwamitin bincike da shugaban hukumar ya naɗa karkashin Daraktan Ayyuka na Musamman a hukumar, Isah Abdullahi, El-Mustapha ya umarci waɗanda aka gayyatar da su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi.
Hukumar ta ce shirya irin waɗannan muhawara ba tare da izininta ba ya saɓa doka kuma zai iya jawo hukunci mai tsanani ga wanda suka karya.
Hukumar ta kuma jaddada ƙudirinta na ci gaba da kula da ayyukan mawaƙan da masu nishaɗantarwa a faɗin jihar tare da yin kira ga jama’a da su zauna lafiya sannan su ci gaba da ba ta haɗin kai a ayyukanta.