Lokacin kadan da ya gabata ne dai aka rufe shahid Sayyid Hassan Nasrallah a makwancinsa na kare dake kusa da filin saukar jiragen sama na Beirut,bayan da aka dauki tsawon yau ana gudanar da jana’izarsa.

Dubun dubatar mutanen Lebanon da kuma wasu daga wajen kasar ne su ka halarci taron jana’izar Sayyid Shahid Hassan Nasrallah da kuma ta Sayyid Hashim Safiyuddin da  aka gudanar a cikin birnin Beirtu.

Tashar talabijin din al’mayadin ta bayyana cewa bisa kirdado adadin mutanen da su ka halarci jana’izar sun kai mutane miliyan daya da 400,000.

Mahalarta jana’izar sun cika filin wasa na birnin Beirut da kuma manyan tituna ta yadda babu masaka cinke, da hakan ya sa motar da take dauke da makararsa da kuma ta Sayyid Hashim Safiyuddin ta rike tafiya a cikin nawa.

An fara gudanar da taron jana’izar ne dai da takaitattun jawabai daga wakilin jagoran juyin musulunci na Iran da kuma na babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Na’im Kassim.

A tsawon lokacin da motar dake dauke da makarar Sayyid Shahid take tafiya an rika watsa jawaban Shahidin da ya yi a lokuta mabanbanta a tsawon rayuwarsa da suke da alaka da yin jinjina ga al’ummar Lebanon,musamman masu bai wa gwgawarmaya kariya da goyon baya.

Lokaci kadan da ya gabata ne dai aka shigar da makarar da take da Sayyid Hassan Nasarallah cikin makwancinsa na karshe, a daidai lokacin da ake karanta suratu Yasin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Hukumar Kula da Yanayi (NiMet), ta sake fitar da gargaɗi game da yiwuwar ambaliyar ruwa a wasu jihohin a daminar bana.

A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, hukumar ta bayyana cewa Jihar Akwa Ibom ce ke fuskantar barazana mafi tsanani a halin yanzu.

Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran

Sauran jihohin da abin ka iya shafa sun haɗa da Sakkwato, Zamfara, Filato, Yobe, Bauchi, Bayelsa, Nasarawa, Binuwai, Ogun, Ekiti, Delta da kuma Ribas.

NiMet ta shawarci al’umma, musamman waɗanda ke zaune a cikin waɗannan jihohin, da su tabbatar sun yashe magudanan ruwa domin bai wa ruwa hanyar wucewa.

Haka kuma ta buƙaci mutane da su nisanci wuraren da ke da hatsarin ambaliya, kuma idan ruwa ya fara ƙarfi, su bar irin waɗannan wuraren domin kare lafiyarsu.

Ambaliya dai na daga cikin manyan matsalolin da ke janyo asarar rayuka da dukiyoyi a Najeriya a duk shekara.

A makonnin baya, garin Mokwa da ke Jihar Neja ya fuskanci ambaliya wadda ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 230.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Jagora: “Yan Sahayoniya Su Saurari Ukuba Mai Tsanani
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari