Sheikh Kassim: Gwagwarmaya Za Ta Ci Gaba Da Dukkanin Karfinta
Published: 23rd, February 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrallah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana Shahidin al’umma Sayyid Hassan Nasrallah da cewa, jagora ne na musamman na al’ummun larabawa da musulmi kuma shugaban gwgawarmaya.
A cikin jawabin da ya gabatar a lokacin jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasrallah, da Shahid Hashim Safiyuddin, inda ya bayyan cewa: A wannan rana muna yin ban kwana da jagora na tarihi na musamman wanda kuma yake a matsayin alkiblar ‘yantattun na duniya.
Babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Sayyid Shahid Hassan Nasrallah ya narke a cikin yi wa musulunci hidima da kuma a cikin riko da wilaya, ya kuwa yi shahada ne a sahun gaba na fagen daga, kuma zai ci gaba da zama a cikin zukatanmu da ruhinmu, za kuma mu yi riko da amana mu ci gaba da tafiya akan wannan tafarkin.
Shekih Na’im Kassim wanda ya yi Magana da sayyid Nasrallah, ya ce: Kai ne kake fadin cewa, tare za mu kammala wannan tafiyar,ko da kuwa za a kashe mu baki daya. Ya Sayyid Nasrallah muna nan akan wannan alkawalin.”
Sheikh Kassim ya kuma ce; Taron da aka yin a jana’iza, yana a matsayin bayyana ra’ayi ne akan riko da gwagwarmaya wanda irinsa ya yi karanci a tarihin Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Sayyid Hassan Nasrallah
এছাড়াও পড়ুন:
An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha
A yau Alhamis ne aka bude bikin baje kolin hada-hadar tattalin arziki da cinikayya na Sin da Afirka karo na hudu a birnin Changsha fadar mulkin lardin Hunan, taron dake kara jaddada himmar kasar Sin ta fuskar karfafa alaka da nahiyar Afirka, nahiyar dake da mafiya yawan kasashe masu tasowa a duniya baki daya.
Kusan kamfanonin Sin da na kasashen Afirka 4,700, da sama da mahalarta 30,000 ne za su halarci bikin na kwanaki hudu, wanda aka yiwa taken “Sin da Afirka: Tunkarar zamanantarwa tare.” Rahotanni daga mashirya bikin na cewa, kwarya-kwaryar darajar ayyukan hadin gwiwa da aka amincewa sun haura dalar Amurka biliyan 11.
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin bude baje kolin, inda kuma ya yi amannar cewa taron zai samar da karin damammaki ga hadin gwiwar Sin da Afirka, tare da haifar da kyakkyawan sakamako.
Wang Yi, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya kara da cewa, duk irin sauyin da aka samu a fannin cudanyar sassan kasa da kasa, Sin za ta ci gaba da tsayawa tsayin daka tare da nahiyar Afirka, za ta samar da kakkarfan tallafi ga ayyukan zamanantar da nahiyar, da kasancewa kawa ta gari, kuma sahihiyar ‘yar uwa ga Afirka kan hanyar nahiyar ta samun ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp