Manufar ita ce a kawo karshen wannan tashin hankalin ta hanyar adalci, mai dorewa, wace dukkanin bangarorin da abin ya shafa za su aminta da ita” in ji Rubio ga menema labarai, duk da cewa babu jami’an Yukiren ko na Turai a wurin tattaunawar.

A wani labarin kuma, shugaban Hadaddiyar Daular Larabawa ya shaida wa Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio cewa kasarsa ba za ta amince da korar Falasdinawa daga Gaza ba.

Mohammed bin Zayed Al Nahyan na mayar da martani ne ga shirin Shugaba Trump na Amurka na karbe ikon Zirin bayan sauya wa al’ummar Gaza matsuguni.

Shugaban na Hadaddiyar Daular Larabawa ya ce sake ginin Gaza abu ne da ya kamata a hada shi da shirin da zai samar da zaman lafiya.

A ci gaba da rangadin da Marco Rubio yake a Gabas ta Tsakiya tuni ya je Isra’ila da Sudiyya.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Rasha

এছাড়াও পড়ুন:

Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai

Rikicin kwamitin gudanarwa da malaman Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Bida (Bida Poly), ya ƙara ƙamari bayan da makarantar ta dakatar da ayyukan Kungiyar Malamai (ASUP) sannan ta kawo sojoji domin kula da jarrabawa da dalibai ke gudanarwa.

Ƙungiyar ASUP reshen kwalejin ta shiga yajin aiki mara wa’adi, domin neman a biya su alawus ɗin ƙarin aiki na watanni 18 da suka wuce.

Ƙungiyar ta umarci mambobinsu da kada su gudanar da jarrabawar zangon da ta fara ranar Litinin, 15 ga Satumba, 2025.

Wani ma’aikacin makarantar ya shaida wa wakilinmu cewa sojojin an gayyace su ne domin kare ɗalibai da wasu malamai daga shirin da ASUP ke yi na hana gudanar da jarrabawa.

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu An kama su kan satar zinarin Naira miliyan 110 a Kebbi

“Ba wai don su gudanar da jarrabawar aka kawo sojojin ba, sai don su kare ɗalibai da malamai daga duk wani cikas. Amma abin mamaki shi ne, me ya sa aka kawo sojoji maimakon ’yan sanda ko Sibil Difens?” in ji shi.

Shugaban ASUP na kwalejin, Kwamared Kolo Joshua, ya tabbatar da komawar su yajin aiki, yana mai cewa gwamnati ta yi biris da haƙƙoƙin malaman.

“Shekaru biyu ke nan muna jurewa, amma yau malaman suna bin bashin watanni 18 na kuɗin ƙarin aiki.

“Duk da tattaunawa da saƙonni da muka aika, ba a ɗauki mataki ba. Sai ma aka dakatar da ƙungiya sannan aka fara tsoratar da shugabanninmu da tambayoyi. Wannan ya jefa malaman cikin rashin kuɗi da raguwar ƙwarin guiwa,” in ji shi.

Ya ce sai dai idan gwamnati ta biya hakkokin malamai da kuma ta koma kan tattaunawa ta gaskiya ne za a samu zaman lafiya a makarantar.

Wata sanarwa da Babban Sakataren Makarantar, Hussaini Mutammad Enagi, ya fitar, ta ce an dakatar da ayyukan ƙungiyar ne bisa dalilin “fargba da kuma rahoton tsaro mai tayar da hankali.”

Sai dai jami’in hulɗa da jama’a na makarantar, Malam Abubakar Dzukogi, ya musanta cewa sojoji aka kawo.

“Na zagaya duk cibiyoyin jarrabawa, ban ga sojoji ba. ASUP ne kawai suka shiga yajin aiki, sai makaranta ta ci gaba da gudanar da jarrabawar. Wannan lamari na farar hula ne, ba na soja ba,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya