HausaTv:
2025-09-17@23:17:11 GMT

Shugabannin Kasashen Larabawa Sun Tattauna Kan Batun Gaza Da Yankin

Published: 22nd, February 2025 GMT

Shugabannin kasashen Larabawa sun tattauna kan batun Gaza dama halin da ake ciki  yankin.

Bisa gayyatar Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman,  an gudanar da taron ‘yan uwantaka na yau da kullun a birnin Riyadh a ranar Juma’a inji kamfanion dilancin labaren kasar na SPA.

Taron ya samu halartar sarki Abdullah II na Jordan, da sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, da shugaban kasar Masar, da Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa hyan, da Sarkin Kuwait Sheikh Meshal Al-Ahmad Al-Jaber Al-Sabah, da kuma Yarima mai jiran gado kuma firaministan kasar Bahrain Yarima Salman bin Hamad Al Khalifa.

 Taron ya ba da damar tuntubar juna kan batutuwa daban-daban na shiyya-shiyya da na kasa da kasa, tare da mai da hankali musamman kan kokarin hadin gwiwa na goyon bayan al’ummar Falastinu da kuma mayar da martani kan abubuwan da ke faruwa a zirin Gaza.

Shugabannin sun yi maraba da gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa da aka shirya gudanarwa a birnin Alkahira na Masar a ranar 4 ga watan Maris, mai zuwa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

Da safiyar yau 17 ga watan Satumba, aka bude dandalin tattauna batutuwan tsaro na Xiangshan karo na 12 da zai dauki kwanaki 3, daga raneku 17 zuwa 19 ga wannan nan, bisa jigon “daukaka tsarin duniya da inganta neman ci gaba cikin lumana”, a nan birnin Beijing.

Tawagogi sama da 100 na gwamnatocin kasashe daban-daban da yankuna da wakilan kungiyoyin kasa da kasa ne ke halartar taron, inda yawan masu rajista ya wuce 1,800.

Da safiyar yau, taron ya shirya tarukan tattaunawa guda 6 bisa jigon “ma’anar cimma nasarar yakin duniya na kin tafarkin murdiyya” da “madaidaitan hanyoyi da manyan kasashe za su bi na yin mu’ammala”, da “hanyoyin warware rikice-rikicen shiyya-shiyya”, da “cika shekaru 80 da kafuwar MDD: samun ci gaba cikin sauye-sauye”, da “amfani da sarrafa sabbin fasahohi”, da kuma “kirkire-kirkire a bangaren kimiyya da fasaha da sauye-sauyen yanayin yaki”. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila