HausaTv:
2025-07-31@19:35:49 GMT

Shugabannin Kasashen Larabawa Sun Tattauna Kan Batun Gaza Da Yankin

Published: 22nd, February 2025 GMT

Shugabannin kasashen Larabawa sun tattauna kan batun Gaza dama halin da ake ciki  yankin.

Bisa gayyatar Yarima mai jiran gado na Saudiyya Mohammed bin Salman,  an gudanar da taron ‘yan uwantaka na yau da kullun a birnin Riyadh a ranar Juma’a inji kamfanion dilancin labaren kasar na SPA.

Taron ya samu halartar sarki Abdullah II na Jordan, da sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, da shugaban kasar Masar, da Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani, na kasar Hadaddiyar Daular Larabawa hyan, da Sarkin Kuwait Sheikh Meshal Al-Ahmad Al-Jaber Al-Sabah, da kuma Yarima mai jiran gado kuma firaministan kasar Bahrain Yarima Salman bin Hamad Al Khalifa.

 Taron ya ba da damar tuntubar juna kan batutuwa daban-daban na shiyya-shiyya da na kasa da kasa, tare da mai da hankali musamman kan kokarin hadin gwiwa na goyon bayan al’ummar Falastinu da kuma mayar da martani kan abubuwan da ke faruwa a zirin Gaza.

Shugabannin sun yi maraba da gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa da aka shirya gudanarwa a birnin Alkahira na Masar a ranar 4 ga watan Maris, mai zuwa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta musanta zargin yin katsalandan a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqa’i, ya musanta zargin katsalandan din Iran a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza.

A yayin da yake amsa tambaya game da ikirarin da shugaban kasar Amurka ya yi na cewa Iran na tsoma baki a shawarwarin tsagaita bude wuta a zirin Gaza, ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da dukkan kasashen duniya tana yin kakkausar suka kan kisan gillar da ake yi a Gaza tare da goyon bayan duk wani tsari da zai kai ga dakatar da aikata laifuka da kuma rage radadin wahalhalun da al’ummar Gaza suke ciki.

Baqa’i ya jaddada cewa; Masu yin shawarwarin Hamas sun fahimci bukatar neman cimma muradun al’ummar Gaza da ake zalunta ta hanyar da ta dace, kuma ba sa bukatar shiga tsakani na bangarori na uku dangane da hakan.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya yi la’akari da katsalandan din Iran a cikin shawarwarin da suka dace da cewa ba shi da tushe balle makama, yana mai jaddada cewa irin wadannan zarge-zarge wani nau’i ne na neman tauyaye hakki da gujewa hakkin da ya rataya a wuyar mutum da kokarin Amurka na gujewa duk wani mugun aiki da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta aikita kan al’ummar Falasdinu, da suka hada da kisan fararen hula 60,000 da ba su ji ba ba su gani ba, da suka hada da mata da kananan yara da kuma killace Zirin Gaza tsawon watanni. Da hana shigar agajin jin kai da kuma kashe fararen hula da ke fama da yunwa da kishirwa a tarkon kisa a wuraren da ake kira cibiyoyin rarraba kayan agaji da wata cibiyar Amurka ta kafa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
  • Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa