Aminiya:
2025-07-31@16:47:24 GMT

Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa

Published: 22nd, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa ƙarin kuɗin makarantar Jami’ar Jihar Gombe (GSU) da kashi 120 cikin 100 ya zama dole domin tabbatar da ɗorewar ingancin ilimi a jami’ar.

Gwamnan ya bayyana haka ne yayin rantsar da kwamitocin gudanarwa na manyan makarantu da hukumomin gwamnati, inda ya jaddada cewa kuɗaɗen makaranta na GSU sun yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da na sauran jami’o’in jihohin makwabta kamar Borno, Adamawa, da Bauchi.

Gwamnatin Yobe za ta gina gadar sama a kan N22.3bn Wasu sassan Abuja za su kasance cikin duhu a ƙarshen mako – TCN

“Muna mayar da hankali sosai kan ilimin firamare da sakandare, amma ilimin manyan makarantu yana da tsada sosai kuma yana buƙatar zuba jari mai tsoka.

“Ƙarin kuɗin da muka yi zai bai wa jami’ar damar ci gaba da bayar da ilimi mai nagarta,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙarin kuɗin makarantar ya samu ne bisa buƙatun ƙungiyar malaman jami’o’i (ASUU) da sauran ƙungiyoyi, domin ƙara kuɗaɗen shiga don inganta jami’ar.

Gwamnan ya buƙaci ɗalibai da iyayensu su yi amfani da shirin lamunin ɗalibai na Gwamnatin Tarayya don samun sauƙin biyan kuɗaɗen makaranta.

“Haƙiƙa, ilimi ba asara ba ne. Ku nemi lamunin ɗalibai domin ku samu damar yin karatu, wanda zai taimaka wa jami’a ta bunƙasa,” in ji Yahaya.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Gombe na bayar da goyon baya sama da sauran jihohi, amma har yanzu akwai buƙatar jami’ar ta nemo wasu hanyoyin samun kuɗaɗe domin tabbatar da ɗorewar ayyukanta da gogayya da sauran manyan makarantu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai Gwamna Inuwa Jami ar Jihar Gombe Kuɗin Makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati

Kwamitin da Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umari Radda, ya kafa domin binciken ayyukan makarantun gaba da sakanadare masu zaman kansu na jihar, ya tabbatar da cewa, 37 cikin 39 ba su da rajista da gwamnati.

Shugaban kwamitin, Farfesa Ahmed Muhammad Bakori, ne ya bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ƙaramar hukumar Bakori da ke jihar.

Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri  Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno

Bakori, wanda shi ne Kwamishinan Harkokin Noma na jihar, ya ce binciken kwamitin ya gano cewa makarantu biyu masu zaman kansu ne kacal a faɗin jihar ke da cikakkiyar rajista da hukumomin da suka dace.

“Jihar Katsina na da makaruntun gaba da sakanadare na gwamnati huɗu da ke bayar da takardar shaidar difloma da koyarwa, sai kuma ƙarin 39 masu zaman kansu.

“Sai dai bincikenmu ya bankaɗo biyu ne kacal a cikin 39 suke da cikakkiyar rajista da hukumomi.”

Kwamishinan, ya kuma ce shida daga cikinsu na buƙatar gyare-gyare domin kammala rajistar, yayin da 22 ke aiki ba tare da rajistar ba.

“Ƙarƙashin sabon tsarin da muka ɗauka yanzu, ya zamo dole makarantun da ke bayar da takardar shaidar digiri su yi rajista da Hukumar Jami’o’i ta Ƙasa (NUC).

“Masu difloma kuma da Hukumar Kula da Ilimin Fasaha (NBTE), sai masu koyarwa da Hukumar Kula da Kwalejin Ilimi ta Ƙasa (NCCE).

Bakori, ya jaddada cewa, duk makarantar da ta saɓa wa wannan tsarin, a shirye gwamnatin take ta rufe ta.

Sai dai ya yi wa ɗaliban da ke makarantun albishir ɗin cewa gwamnatin za ta tabbatar ta sauya musu makaranta zuwa masu rajista daga waɗanda ba su da su, idan buƙatar rufe su ta taso.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja