Dalilan ƙara kuɗin Jami’ar Gombe — Gwamna Inuwa
Published: 22nd, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana cewa ƙarin kuɗin makarantar Jami’ar Jihar Gombe (GSU) da kashi 120 cikin 100 ya zama dole domin tabbatar da ɗorewar ingancin ilimi a jami’ar.
Gwamnan ya bayyana haka ne yayin rantsar da kwamitocin gudanarwa na manyan makarantu da hukumomin gwamnati, inda ya jaddada cewa kuɗaɗen makaranta na GSU sun yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da na sauran jami’o’in jihohin makwabta kamar Borno, Adamawa, da Bauchi.
“Muna mayar da hankali sosai kan ilimin firamare da sakandare, amma ilimin manyan makarantu yana da tsada sosai kuma yana buƙatar zuba jari mai tsoka.
“Ƙarin kuɗin da muka yi zai bai wa jami’ar damar ci gaba da bayar da ilimi mai nagarta,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa ƙarin kuɗin makarantar ya samu ne bisa buƙatun ƙungiyar malaman jami’o’i (ASUU) da sauran ƙungiyoyi, domin ƙara kuɗaɗen shiga don inganta jami’ar.
Gwamnan ya buƙaci ɗalibai da iyayensu su yi amfani da shirin lamunin ɗalibai na Gwamnatin Tarayya don samun sauƙin biyan kuɗaɗen makaranta.
“Haƙiƙa, ilimi ba asara ba ne. Ku nemi lamunin ɗalibai domin ku samu damar yin karatu, wanda zai taimaka wa jami’a ta bunƙasa,” in ji Yahaya.
Ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Gombe na bayar da goyon baya sama da sauran jihohi, amma har yanzu akwai buƙatar jami’ar ta nemo wasu hanyoyin samun kuɗaɗe domin tabbatar da ɗorewar ayyukanta da gogayya da sauran manyan makarantu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai Gwamna Inuwa Jami ar Jihar Gombe Kuɗin Makaranta
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kakkausan martanin da Iran ta mayar ya tabbatar da cewa babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani ba
Izzat al-Rishq mamba na ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya jaddada cewa: Kakkausan martanin da Iraniyawa suka mayar ya tabbatar da cewa; babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani kan zaluncinsa ba, kuma babu wuce gona da iri ba tare da hukunci ba.
Izzat al-Rishq ya yi nuni da cewa: Tabbas makamai masu linzami da jiragen saman yaki marasa matuka ciki na Iran sun yi nasarar kai wa cikin tsakiyar haramtacciyar kasar Isra’ila, duk kuwa da kace-nacen da ake yi na girke na’urorin kakkabo makamai a haramtacciyar kasar Isra’ila musamman Iron Dome, Arrow da David’s Sling.
Al-Rashq ya kuma bayyana cewa: Tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila ya gaza shawo kan hare-haren da Iran suka kai, kuma a halin yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila tana fama da gobarar da ta kunna a tsakanin al’ummomin yankin. A karshe ya jaddada cewa: Sakon a bayyane yake: Duk wanda ya yi tsokana, to tantana kudarsa.