Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.
Published: 19th, February 2025 GMT
Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za ta gudanar da bikin tunawa da Sir Ahmadu Bello na shekara karo na 11 a ranar Litinin, 24 ga Fabrairu, 2025, a Bauchi, Jihar Bauchi.
Taron, wanda aka shirya tare da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Bauchi, zai girmama marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato kuma Firaministan tsohuwar Yankin Arewa.
A bana, taken laccar shi ne “Arzikin Halitta: Juya Albarkatun Yankin Arewa Zuwa Ci Gaban Tattalin Arziki Mai Dorewa.”
Tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan yadda za a yi amfani da albarkatun noma da ma’adanai da ruwa don bunkasa ci gaban tattalin arzikin yankin.
Duba da kalubalen tattalin arzikin da Najeriya ke fuskanta, musamman yankin Arewa, laccar za ta bayyana rawar da gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu da kungiyoyin al’umma za su taka wajen inganta sarrafa albarkatu da bunkasa darajar kayayyaki da samar da ayyukan yi.
Babbar lacca za a gabatar da ita ne daga bakin Dr. Mansur Mukhtar (Sarkin Bai Kano), tsohon Mataimakin Shugaban Bankin Musulunci kuma Shugaban Bankin Masana’antu na Najeriya.
Ana sa ran Sanata George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance Babban Bako na Musamman a wurin taron.
Haka nan, ana sa ran halartar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, kuma zai jagoranci taron.
Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, zai kasance Babban Mai Masaukin baki. Haka kuma, ana sa ran halartar gwamnonin jihohi da ministoci da ‘yan majalisa da sarakuna da sauran manyan baki daga sassa daban-daban.
A cewar Darakta-Janar na Gidauniyar, Injiniya Dr Abubakar Gambo Umar, albarkatun yankin Arewa na da babban damar sauya tattalin arzikin yankin.
“Sai dai dole mu dauki matakan da za su tabbatar da sarrafa albarkatunmu cikin adalci da dorewa, domin amfanin kowa da kowa,” in ji shi.
A yayin taron, gidauniyar za ta bayar da tallafin karatu ga dalibai marasa galihu daga Jihar Bauchi da ke karatu a manyan makarantu domin tallafa musu.
Bugu da kari, za a karrama wasu fitattun mutane da lambar yabo saboda gudunmawar da suka bayar ga cigaban al’umma.
Har ila yau, za a gudanar da shirin ba da agajin lafiya domin samar da hidimar kiwon lafiya ga al’ummar yankin.
Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello an kafa ta ne domin ci gaba da girmama gadon shugabanci da ilimi da ci gaban tattalin arziki da marigayi Sardaunan Sakkwato ya assasa.
Bikin tunawa na kowace shekara, wanda ke gudana a jihohi 19 na Arewa, na zama wata kafa ta tattaunawa kan ci gaban yankin da shugabanci.
Gidauniyar ta nemi afuwar duk wani rashin jin dadi da sauya ranar taron ka iya haifarwa, tare da gode wa duk masu mara mata baya.
Rel: Khadija Kubau
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Karo Taronta Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello yankin Arewa Jihar Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-haren HKI da Amurka a yankin yammacin Asiya ya kara rashin zamn lafiya a yankin.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadin haka ne a lokacinda yake zantawa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Girka a jiya talata . Ya kuma kara da cewa hare-haren sun yu watsi da hanyar zaman lafiya da kuma zaman lumana a yankin. Ya kuma yi sanadiyyar karin tashe tashen hankula a yankin.
Ministan ya bukaci kasashen duniya gaba daya su yi tir da HKI da kuma Amurka wadanda suka keta hurumin kasa mamba a MDD ba tare da wani daloli nay an haka ba. Ya ce hare-haren da kasashen biyu suka kaiwa JMI wanda ya cinye rayukan mutane da dama ya sabawa kudurin MDD ta 2231, wanda hakan barazana ce ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa.
Ministan ya kara da cewa wadannan hare-hare sun zo ne a dai-dai lokacinda Iran da Amurka suna kan teburin tattaunawa don fahintar juna kan shirin Nukliyar kasar. Wanda haka yin watsi da hanyar diblomasiyya da kuma zaman lafiya ne.
Daga karshe ministan ya bayana cewa ayyukann ta’addanci wanda HKI take aikatawa a Gaza shi ne yake kunna wutan fitina a yankin da kuma duniya gaba daya.
A nashi bangren ministan harkokin wajen kasar Girka ya ce, yana mika ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu a wadannan hare-hare sannan yana fatan tsagaita wutan da aka samu zai dore. Ya kuma nuna damuwarsa da abinda yake faruwa a gaza kan falasdinawa musamman rashin barin abinci ya shiga yankin.