’Yan bindiga sun Kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja
Published: 19th, February 2025 GMT
’Yan bindiga sun kashe mutum biyu tare da yin awon gaba da aƙalla wasu 10 a hare-haren da suka kai Ƙananan Hukumomin Wushishi da Rafi a Jihar Neja.
Wani jami’in tsaro da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa Aminiya cewa waɗanda aka kashe sun haɗa da ɗan sa-kai da wani mutum mai saran itace.
Hana Biza: Najeriya ta cancanci a girmama ta – Babban Hafsan Tsaro Rayuka 10 da dukiyar N11bn sun salwanta yayin zanga-zangar tsadar rayuwa a KanoHar ila yau, ya ce wani ɗan sa-kai na daga cikin waɗanda aka sace.
“A halin yanzu, ’yan bindiga suna cikin dajin Akare. Sun sace ɗaya daga cikin ‘yan sa-kai, kuma yana da bindigogi biyu a tare da shi lokacin da suka yi awon gaba da shi.
“Ba mu san abin da za mu yi a yanzu ba. Mun shafe tsawon ranar ɗaya muna fafatawa da su. An kashe ɗaya daga cikin ’yan sa-kai da kuma wani mai saran itace,” in ji shi.
Mazauna yankin sun bayyana cewa har kawo hanzu ’yan bindigar suna cikin dajin tare da shanun da suka sace a yankin.
An ruwaito cewa sun kama mai saran itacen, tare da tilasta masa ya nuna musu hanya, sannan suka harbe shi.
Wasu majiyoyi sun bayyana cewa jami’an tsaro da ’yan sa-kai na ci gaba da ƙoƙarin bin sahun ‘yan bindigar.
Wani mazaunin yankin ya ce, “Mun ga ’yan bindigar suna tafiya da babura, uku-uku a kan kowanne.
“Suna wucewa ta wajen da suka saba bi a Kundu, a Ƙaramar Hukumar Rafi, sun nufin Ƙaramar Hukumar Mashegu tare da shanun da suka sace.”
Wani mazaunin Ƙaramar Hukumar Rafi, ya ce ’yan bindigar sun kuma kai hari wasu ƙauyuka a gundumar Gunna da safiyar ranar Laraba, inda suka ƙone rumbunan doya.
Da yake tabbatar da harin, Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar Neja, Birgediya Janar Bello Abdullahi Mohammed (mai ritaya), ya ce, an tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin.
“An riga an tura jami’an tsaro zuwa yankin, kuma suna bin sahun ’yan bindigar.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hari yan bindigar
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mafarauta 10 a Adamawa
Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.
Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalA cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.
Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.
“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.
Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.
“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”
Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.
Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.