Aminiya:
2025-05-01@04:12:43 GMT

Jirgin soji ya kashe fararen hula a Katsina

Published: 17th, February 2025 GMT

Wani jirgin sojin Najeriya ya jefa wa fararen hula bom inda ya kashe fararen hula bakwai a yankin Yani  da ke Ƙaramar Hukumar Safana ta Jihar Katsina.

Mamatan sun hada da mutum shida ’yan gida ɗaya, kamar yadda wani shaida ya bayyana.

Hakan na zuwa ne bayan wasu jami’an tsaro da suka hada da ’yan sanda biyu da wani jami’in Rundunar Tsaron Al’umma na jihar (CWC) sun kwanta dama a yayin musayar wuta da ’yan bindiga a Ƙaramar Hukumar a ranar Asabar.

Wani mazaunin Gundumar Zakka da ke Ƙaramar Hukumar, yankin da abin ya faru, ya bayyana cewa an yi arangamar ne bayan zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a jihar ranar Asabar, inda ’yan bindiga suka shirya kai wa masu zaɓe hari a kauyen Zakka.

Bayan samun rahoton shirin harin ne jami’an tsaron suka je domin daƙile ’yan bindigar, inda a garin haka aka yi musayar wuta tsakanin bangarorin. Wani hafsan dan sanda da jami’in CWC sun rasu, daga bisani wani ɗan sanda da ya ji rauni a arangamar ya cika.

Ya bayyana cewa, “bayan nan ne wani jirgin soji ya zo, watakila domin kai wa jami’an tsaron ɗauki. A nan ne ya jefa bom a yankin Yani da ke ƙauyen Zakka, wanda ya halaka  mutum shida ’yan gida ɗaya, ya kuma jikkata wata mata.”

Wannan ba shi ne karon farko ba da jirgin soji ya kai wa fararen hula hari ba a Ƙaramar Hukumar ta Safana.

A watan Yulin shekara ta 2022 wani jirgin soji ya jefa bom a yankin Kunkumi da ke Ƙaramar Hukumar ta Safana, inda ya kashe aƙalla mutum biyu tare da jikkata wasu tara.

Wakilinmu ya yi duk ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sanda da sojoji da ke jihar game da lamarin, amma hakan ya faskara.

Amma dai kafar yaɗa labarai 4 Deutsche Welle (DW) ta ruwaito labarin harin, tana mai ambato wasu shaidu da suka tabbatar da aukuwarsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Ƙaramar Hukumar jirgin soji ya fararen hula

এছাড়াও পড়ুন:

Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa

Wata koutun soja ta yanke wa wani jami’inta hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun sa da laifn kashe buduwarsa.

Kotun da ta zauna a Hedikwatar Runduna ta 82 da ke Enugu, ta yanke wa Private Adamu Mohammed hukuncin kisa kan laifin budurwar taas mai suna Hauwa Ali.

Da yake sanar da hukuncin, Shugaban kotun, Birgediya Sadisu Buhari, ya ce, “Kotun Soja ta Kasa ta yanke hukuncin cewa sojan da ake tuhuma, mai lamba 21NA/80/6365 Private Adamu Mohammed, an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa tuhumar kisan kai.”

Mukaddashin kakakin Rundunar, Jonah Unuakhalu, ya ce kwamitin kotun  ya cimma matsaya ɗaya bayan nazari mai zurfi na shaidu, tarihin aikin wanda ake tuhuma, da kuma roƙon sassauci daga lauyansa.

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno

Ya shaida wa manema labarai a Abuja cewa kotun sojan, ta kuma yanke wa wani Soja mai suna Private Abubakar Yusuf hukuncin ɗaurin shekaru 10 a kurkuku saboda samun sa da laifin fashi da makami a wani shahararren kantin sayayya a Enugu.

Ya kara da cewa an yanke wa waɗannan mutane biyu hukuncin ne bayan kammala shari’o’insu kan laifukan kisan kai da fashi da makami.

Babban Kwamandan Runduna ta 82, Manjo-Janar Oluyemi Olatoye, ne ya kaddamar da kotun sojin a ranar 18 ga Fabrairu, 2025, domin yanke hukunci kan shari’o’in da suka shafi ma’aikatan da suka yi kuskure a cikin Rundunar.

A cewarsa, waɗannan hukunce-hukuncen sai sun samu tabbatarwa daga hukumomin soji da suka dace, wanda ya nuna ƙarshen shari’o’in sojojin.

Ya sake jaddada ƙudurin Sojojin Najeriya na tabbatar da ɗa’a da kuma kiyaye mafi girman ƙa’idoji na ɗabi’u da ƙwarewa.

“Kuskuren ayyukan wasu kaɗan ba su nuna ƙimar ƙungiyar ba. A koyaushe ana ɗaukar matakai masu sauri da kuma ƙarfi don tabbatar da riƙon amana da adalci,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi