HKI Ba Zata Yarda A Kafa Kasar Palasdinu Ba, Saboda Barazana Ce Ga Wanzuwar HKI
Published: 17th, February 2025 GMT
Ministan tsaron HKI Israel Katz ya bayyana cewa gwamnatin HKIba zata bar a kafa kasar Falasdinu ba, saboda hakan barazana ce ga samuwar HKI.
Israek Kazt ya bayyana haka ne a lokacin ganawar jami’an gwamnatin HKI da tawagar kasar Amurka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a taron su da tawagar kasar ta Amurka a yau.
Wasu kafafen yada labarai sun nakalto wasu manya manyan jami’an sojojin kasar suna tunanin dakatar da tsagaita wuta da suka kulla da Hamas. Banda haka suna ganin shawarar shugaba kasar Amurka Donal Trump n araba gaza da Falasdinawa ne kawai zai tabbatar da wanzuwar HKI.
Kafin haka dai Banyamin Natanyahu ya fadawa kafafen yada labarai kan cewa Falasdinawa suna da damar su bar Gaza su je inda suka ga dama, idan sun bukaci hakan, amma idan bas u yi ba, to mai yuwa a kashesu gaba daya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
Iran ta yi Allah-wadai da wani kuduri da ta danganta da na siyasa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta dauka, tana mai cewa ba shi da tushe na fasaha ko doka.
Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) da ma’aikatar harkokin wajen kasar sun fitar da sanarwar hadin gwiwa yau Alhamis bayan da majalisar gwamnonin hukumar ta IAEA suka amince da wani kuduri da ke zargin Iran da rashin cika alkawuran da ta dauka na nukiliya.
Kuri’u 19 ne suka amince da kudurin wanda Amurka da Birtaniya da Faransa da Jamus suka tsara.
Kasashen Rasha, China da Burkina Faso sun kada kuri’ar kin amincewa da shi, Yayin da kasashen Afirka ta Kudu, Indiya, Pakistan, Masar, Indonesia da Brazil suka ce su kam ba ruwan su.
Sanarwar da Iran ta fitar dangane da wannan kudiri ta ce, Jamhuriyar Musulunci ba ta da wani zabi face mayar da martani ga wannan kudiri na siyasa.”
Sanarwar ta ce, Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI), Mohammad Eslami, ya ba da umarnin gina sabuwar cibiyar tace uranium a wani wuri mai aminci.
Sabuwar cibiyar za ta kunshi sabbin na’urorin tace uranium na zamani inji sanarwar.
A cikin sanarwar, Tehran ta yi tir da kudirin na “siyasa da son zuciya” na IAEA Wanda Amurka da manyan kasashen Turai uku – Faransa, Jamus da Birtaniya suka tsara.
Iran ta kuma yi tir da shirun da Amurka da kawayenta na Turai suka yi wajen tinkarar yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kin mutunta yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka tabbatar da sake ganawa a karo na shida a ranar Lahadi mai zuwa game da shirin nukiliyar Iran wanda a’a gudanar a birnin Muscat a shiga stakanin kasar Oman.