Ƙasashen da suke da saukin cin hanci a duniya

Mafi yawan kasashen da rahoton ya nuna cewa babu yawaitar matsalar cin hanci da rashawa suna a nahiyar Turai ne.

Bakwai daga cikin kasashen 10 na farko, wadanda ba su da matsalar Rasha duk a yankin Tarayyar ta Turai suke.

Qasar da ta fi kowace a duniya samun maki a bangaren yaki da rashawa ita ce Denmark, wadda take da maki 90.

Sai kuma Finland mai maki 88, ta uku kuma ita ce Singapore, wadda ke a kudu maso gabashin nahiyar Asiya.

Ga yadda kasashen 10 na farko suka kasance:

1. Denmark – Maki 90

2. Finland – Maki 88

3. Singapore – Maki 84.

4. New Zealand – Maki 83.

5. Ludembourg – Maki 81.

6. Norway – Maki 81.

7. Swtizerland – Maki 81

8. Sweden – Maki 80.-

9. Netherlands – Maki 78-

10. Austria – Maki 77.

Sai dai rahoton na Tranparency International ya ce duk da cewa kasashen Turai su ne suka fi samun yabo a rahoton, to amma makin da suke samu ya ragu cikin shekara biyu a jere.

Rahoton ya ce wasu shugabannin kasashen na Turai sun mayar da hankali wajen “abin da zai dadada wa harkar kasuwanci kawai a maimakon abubuwan da za su inganta rayuwar al’umma”.

Ƙasashen da ke kurar-baya

Rahoton ya nuna cewa akasarin kasashen da ke kasan jadawalin suna a nahiyar Afirka ne, inda nahiyar ke da kasashe shida cikin 10 da suka samu maki mafi karanci.

Sauran kasashen sun fito ne daga nahiyar Amurka ta kudu sai kuma Gabas ta takiya.

Sudan ta Kudu da Somaliya su ne kasashen da ke kasan tebur, inda Sudan ta Kudu ke da maki 8 kacal yayin da Somaliya ke da maki 9.

170. Sudan – Maki 15 –

172. Nicaragua – Maki 14-

173. Ekuatorial Guinea – Maki 13

173. Eritriya – Maki 13-

173. Libya – Maki 13-

173.Yemen – Maki 177. Syriya – Maki 12 –

178. Venezuela – Maki 10-

179. Somaliya – Maki 9-

180. Sudan ta Kudu – Maki 8

Rahoton ya ce nahiyar Afirka, kudu da hamadar sahara ce ta samu maki mafi karanci. Hakan ya faru ne sanadiyyar rikice-rikice masu alaka da sauyin yanayi wadanda ke tarnaki ga ci gaban yankin.

Sai dai rahoton ya ce bunkasar yaki da rashawa a Gabas ta Tsakiya da Arewacin Amurka wani abu ne na farin ciki, sai dai wannan ne karo na farko da aka samu haka a cikin shekara 10, kuma ci gaban da maki daya ne kacal.

Mene ne matsayin Nijeriya da Nijar da Ghana?

A tsakanin Nijeriya da Nijar da Ghana, Ghana ce ta fi tabuka abin kirki, inda take a matsayi na 80 bayan samun maki 40.

Sai Jamhuriyar Nijar, wadda take a matsayi na 107 bayan samun maki 34.

Nijeriya na a matsayi na 140 inda ta samu maki 26, tare da wasu kasashen kamar Medico da Iraki da Kamaru.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Rashawa

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Ba tare da saninmu ba, yawancin al’ummar Afirka musamman ma naYammacin Afirka suna fama da abinda ake kira da suna irin hali ko yanayin da aka shiga sanadiyar lamarin cinikin Bayi.Bayan shekara 100 da aka yi daga shekarar 1801 zuwa 1901, an yi wani kokarin da ake yi ma kallon tamkar wani takune na yadda za’a kubuta daga irin cin fuskar da ake yi kowace rana.

Kafin dai a tsunduma sosai cikin lamarin cinikin Bayi, yana da matukar kyau a fara yin bayani kan yadda abin ya fara:Lamarin cinikin Bayi ba manufa bace ta Yammacin Turai.Duk lamarin ya zarce wani hasashen da za’a iya yi ko wani rubutun,da aka yi aka aje.Idan kuma aka duba ta bangaren nahiyar Afirka ita kanta, sha’anin cinikin Bayi ya kasance nae kafin zuwa Turawa shekaru darurra da suka gabata,lamarin kuma yana ci gaba har zuwa halin da ake ciki yanzu ,ana iya tunawa da yadda Bayin da aka saya a nahiyar Afirka ake tafiya da su ta hanyar Sahara wadda take da Yashi,ta haka ne aka fara musanyar mutane,a bada su ,sannan a amshi wasu abubuwa”.

Afirka, a matsayinta na nahiya ita ma ta dandana kudarta idan ana maganatr cinikin Bayi har zuwa shenture 14 wanda ya zarce shekara 1000 ke nan:10 ga duniyar Larabawa,sai kuma 4 ga sauran yammacin Turai. Ciniki Bayi na bangaren Larabawa ya far ne a karni na 8 hakan ta kasance ne saboda yadda addinin musulunci ya hana Musulmai daga bautar da ‘yan’uwansu. Duk da an hana hakan bukatar mutane su rika yin wasu ayyuka,don haka shi yasa Larabawa suke zuwa nahiyar Afirka domin su samu Bayin.Da farko sun tsaya ta gabas ta gabar ruwa na, Rift Balley, amma yayin da suke kasuwanci, sai suka rika yada addininsu na musulunci. Wannan ya nuan ke nan wurin da yake ana ta lamarin fataucin Bayi,ya zama yanzu babu yadda za su yi su samu Bayi daga can,don haka sannu a hankali sai suka maida akalarsu zuwa yammacin Afirka.domin idon su ya fara budewa saboda ai addinin musulunci ya hana cinikin Bayi. Wannan shi yake nuna duk yadda Larabawa suke bukatar samun ‘yan Afirka a matsayin Bayi ya zo karshe.

Abu daya wanda yake kamar sun yi kama da juna tsakaanin Larabawa da Yammacin Turai shi ne suna yin amfani ne da addini, Musulunci da Kiristanci domin su samu bakin bada dalilin da yasa suke kasuwancin mutane.A kokarin da muke na nuna yin kama da juna, sai mun yi bayani dangane da bambancin, tsakanin kasuwancin na hanyar da ake bi ta Yashi, da kuma ta wani babban Kogi da kuma na ake bi ta babban ruwa ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49