Nijeriya Na Jerin Ƙasashen Da Cin Hanci Da Rashawa Suka Yi Wa Katutu A 2024 -Rahoto
Published: 16th, February 2025 GMT
Ƙasashen da suke da saukin cin hanci a duniya
Mafi yawan kasashen da rahoton ya nuna cewa babu yawaitar matsalar cin hanci da rashawa suna a nahiyar Turai ne.
Bakwai daga cikin kasashen 10 na farko, wadanda ba su da matsalar Rasha duk a yankin Tarayyar ta Turai suke.
Qasar da ta fi kowace a duniya samun maki a bangaren yaki da rashawa ita ce Denmark, wadda take da maki 90.
Sai kuma Finland mai maki 88, ta uku kuma ita ce Singapore, wadda ke a kudu maso gabashin nahiyar Asiya.
Ga yadda kasashen 10 na farko suka kasance:
1. Denmark – Maki 90
2. Finland – Maki 88
3. Singapore – Maki 84.
4. New Zealand – Maki 83.
5. Ludembourg – Maki 81.
6. Norway – Maki 81.
7. Swtizerland – Maki 81
8. Sweden – Maki 80.-
9. Netherlands – Maki 78-
10. Austria – Maki 77.
Sai dai rahoton na Tranparency International ya ce duk da cewa kasashen Turai su ne suka fi samun yabo a rahoton, to amma makin da suke samu ya ragu cikin shekara biyu a jere.
Rahoton ya ce wasu shugabannin kasashen na Turai sun mayar da hankali wajen “abin da zai dadada wa harkar kasuwanci kawai a maimakon abubuwan da za su inganta rayuwar al’umma”.
Ƙasashen da ke kurar-baya
Rahoton ya nuna cewa akasarin kasashen da ke kasan jadawalin suna a nahiyar Afirka ne, inda nahiyar ke da kasashe shida cikin 10 da suka samu maki mafi karanci.
Sauran kasashen sun fito ne daga nahiyar Amurka ta kudu sai kuma Gabas ta takiya.
Sudan ta Kudu da Somaliya su ne kasashen da ke kasan tebur, inda Sudan ta Kudu ke da maki 8 kacal yayin da Somaliya ke da maki 9.
170. Sudan – Maki 15 –
172. Nicaragua – Maki 14-
173. Ekuatorial Guinea – Maki 13
173. Eritriya – Maki 13-
173. Libya – Maki 13-
173.Yemen – Maki 177. Syriya – Maki 12 –
178. Venezuela – Maki 10-
179. Somaliya – Maki 9-
180. Sudan ta Kudu – Maki 8
Rahoton ya ce nahiyar Afirka, kudu da hamadar sahara ce ta samu maki mafi karanci. Hakan ya faru ne sanadiyyar rikice-rikice masu alaka da sauyin yanayi wadanda ke tarnaki ga ci gaban yankin.
Sai dai rahoton ya ce bunkasar yaki da rashawa a Gabas ta Tsakiya da Arewacin Amurka wani abu ne na farin ciki, sai dai wannan ne karo na farko da aka samu haka a cikin shekara 10, kuma ci gaban da maki daya ne kacal.
Mene ne matsayin Nijeriya da Nijar da Ghana?
A tsakanin Nijeriya da Nijar da Ghana, Ghana ce ta fi tabuka abin kirki, inda take a matsayi na 80 bayan samun maki 40.
Sai Jamhuriyar Nijar, wadda take a matsayi na 107 bayan samun maki 34.
Nijeriya na a matsayi na 140 inda ta samu maki 26, tare da wasu kasashen kamar Medico da Iraki da Kamaru.
কীওয়ার্ড: Rashawa
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA