Gwamnatin Amurka Ta na Son Katse Dangantakan Da Ke Tsakanin Rasha Da Iran
Published: 16th, February 2025 GMT
Jakadan Amurka na musamman kan kasashen Rashad Ukraine ya bayyana cewa Amurka tana kokarin ganin ta kawo karshen dukkan dangantakar da ke tsakanin kasashen China da Rasha da kuma JMI.
Tashar talabijian ta Presstv a nan Tehran ta nakalto, Keith Kellogg ya na fadar haka a taron Munich na tsaro a jiya Asabar.
Ya kuma kara da cewa gwamnatin Trump tana aiki dare da rana don ganin ta wargaza dukkan dangantaka da ke tsakani Iran da Rasha da kuma China.
Jakadan ya kara da cewa dangantaka da ke tsakanin wadannan kasashen da JMI babu ita a shekaru 4 da suka gabata. Amma shugaba Donal Tromp yana aiki a kan haka. don ganin an katse dangantakar wadannan manya-manyan kasashe da JMI. Saboda barin Iran ita kadai.
Manufar dai ita ce tabbatar da cewa duk kasashen duniya sun maida Iran saniyar ware.
A sannan ne kuma takunkuman tattalin arziki mafi tsananin da gwamnatin Trump ta dorawa JMI zasu yi aiki. A sannan ne gwamnatin kasar Iran zata durkusar.
Kasar Iran dai tana da dangantaka ta musamman kuma masu dogon zango da wadannan kasashe biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
Gwamnatin Jigawa ta amince da sabon tsarin ka’idojin aiki domin aiwatar da shirin kula da lafiyar mata masu juna biyu, da jarirai da ƙananan yara kyauta a cibiyoyin lafiya na jihar.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana haka bayan zaman majalisar zartarwa da aka gudanar a gidan gwamnati Dutse.
Ya ce ka’idojin za su taimaka wajen inganta nagartar hidima, fayyace karewar ma’aikata, da kuma tabbatar da gaskiya, da bin doka da tsari a asibitoci.
Kwamishinan ya ƙara da cewa matakin ya dace da manufar gwamnatin jihar na rage mace-macen mata da yara da kuma tabbatar da samun ingantacciyar kulawa ga kowa.
Ya ce za a fara aiwatar da tsarin nan take, tare da horas da shugabannin asibitoci da cibiyoyin lafiya na ƙananan hukumomi domin cimma nasarar shirin .
Usman Muhammad Zaria
—
Kana so in ƙara ɗan salo na labarin jarida (irin rubutun kafafen yaɗa labarai) ko a barshi haka cikin sauƙin bayani?