Amurka : Trump Da Putin Za Su Tattauna Kan Ukraine, Nan Ba Da Jimawa Ba
Published: 13th, February 2025 GMT
Gwamnatin Washington, ta sanar da cewa nan ba da jimawa ba shugaban kasar Donald Trump da takwaransa na Rasha Vladimir Putin, zasu fara tattaunawa kan batun Ukraine da nufin tsagaita wuta don kawo karshen yakin da kasashen biyu ke yi ta hanyar tattaunawa.
Shugaban na Amurka ya sanar a ranar Laraba cewa ya yi doguwar tattaunawa da takwaransa na Rasha, kuma shugabannin biyu Shugabannin biyu sun shirya ganawa a karon farko a kasar Saudiyya.
Donald Trump da Vladimir Putin sun amince su “yi aiki tare sosai” tare da fara tattaunawa “nan da nan” kan Ukraine.
Kremlin ta tabbatar da cewa tana son “magance rikicin Ukraine ta hanyar “tattaunawar zaman lafiya”.
Tattaunawar ta wayar tarho tsakanin Donald Trump da Vladimir Putin a ranar Laraba, ta yi tasiri, a cewar washington.
Shugaban na Amurka ya bayyana cewa, “Mun amince da yin aiki tare, gami da ziyartar juna a kasashen.”
Kakakin fadar Kremlin Dmitry Peskov ya shaidawa manema labarai cewa Vladimir Putin ya shaidawa shugaban Amurka cewa yana son a samar da mafita a rikicin Ukraine ta hanyar “tattaunawar zaman lafiya.” Ta hanyar magance musabbabin rikicin,” in ji shi.
A cewar Dmitry Peskov, Vladimir Putin “ya gayyaci Donald Trump ya ziyarci Moscow kuma ya bayyana shirinsa na karbar jami’an Amurka a Rasha.” Kuma duka biyun “sun amince da ci gaba da tuntuɓar juna, gami da gudanar da taruruka.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar
Gwamnatin Najeriya ta mayar da martani kan jawabin da shugaban Amurka Donald Trump ya yi inda yake zargin kashe kiristoci a Najeriyar.
A martanin da ta mayar, ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, ta ce lamarin ba haka ba ne.
Sanarwar da kakakin ma’aikatar Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya sanya wa hannu, ta ce, “duk da cewa Najeriya na godiya da kulawar da kasashen duniya ke ba ta musamman kan batun hakkin dan’adam da hakkin addini, wannan batun na zargin kashe kiristoci a kasar ba haka ba ne.
Duk yan Najeriya suna da yancin gudanar da addininsu yadda ya kamata, kuma suna gudanar da ibadarsu ba tare da tsangwama ba.” Inji sanarwar.
Shi dai shugaban Amurka Donald Trump Ya ce kiristanci na fuskantar babbar barazana a Najeriya,”, inda ya kara da cewa ana kashe dubban Kiristoci, kuma masu tsaurin kishin Islama ne ke aikata wannan kisan gillar.
“Saboda haka ya ayyana Najeriya kasar da ake da damuwa a kanta.”
Bugu da ƙari, Trump ya ce ya bai wa ‘yan majalisar wakilai Riley Moore da Tom Cole umarnin fara bincike kan hakan kuma su kai masa rahoton sakamakonsa.
Gwamnatin Najeriya dai ta ce za ta ci gaba da tattaunawa da Amurka da kasashen duniya domin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci