Mutanen Najeriya suna  bayyana fushinsu akan kara kudaden sayen cajin shiga kafar sadarwa na Internet –Data- da manyan kamfanoni irin su MTN da Airtel su ka yi, saboda yadda ake fama da matsalar rayuwa.

Kamfanin MTN shi ne mafi girma a tsakanin kamfanonin samar da hidimomi na hanyar sadarwa, inda a yanzu ake sayar da Giga 15, akan Naira 6,000 bayan da a baya take naira 2,000 ( wato daga dala 1.

33-3.99) da hakan yake nufin cewa an rubanya farashin sau uku.

Shi ma kamfanin Airtel ya kara yawan kudaden cajin nashi da kaso mai yawa.

Wannan Karin da kamfanonin su ka yi, ya bakanta ran masu amfani da su, musamman a wannan lokacin da ake fama da yanayi mai tsanani na  tattalin arziki.

Kamfanin MTN ya wallafa sanarwa a shafinsa na X cewa; Karin kudin ya zama wajibi domin gabatar da hidimomi  masu nagarta ga kwastomominsa, tare da neman gafara ga abokan hulda.

Wani daga cikin masu tofa albarkacin baki akan Karin na MNT; ya walllafa cewa; Rubanya kudi har sau uku? Lallai karshen duniya ya zo.”

Ana hasashen cewa Karin da aka yi zai shafi kananan ‘yan kasuwa da suke dogaro da hanyoyin sadarwar masu saukin kudi domin tafiyar da harkokinsu.

Ya zuwa yanzu dai kamfanin Globacom, da shi ne kamfani na uku mafi grima a cikin kasar, bai yi  Karin kudin ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje

Shugaban kasar Iran ya nuna murnarsa da yin maraba lalai da masu zuba hannun jari daga kasashen waje a Iran

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana Iran a matsayin dandalin da ta dace wajen zuba hannun jari da gudanar da harkar kasuwanci, yana maraba da masu zuba hannun jari na kasashen waje da ‘yan kasuwa na duniya da su shiga harkokin tattalin arziki da zuba hannun jari a Iran.

A yayin bikin bude baje koli karo na bakwai na baje kolin kayayyakin da Iran ke fitarwa zuwa kasashen ketare (Iran Expo 2025) a safiyar yau Litinin, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi maraba da baki na kasashen waje da suka halarci wannan baje kolin, yana mai cewa, “Ko da yake ana gabatar musu da wani hoto na daban da ya yi hannun riga da hakikanin Iran da al’ummar kasarta a ketare, amma Iran kasa ce mai karbar baki, kuma al’ummarta masu tausayi da nuna jin kai.”

Yana mai jaddada cewa: Iran wata kafa ce da ta dace da zuba hannun jarin kasuwanci da yawon bude ido na ketare, Pezeshkian ya bayyana cewa da wannan karfin, kuma ta hanyar ciniki, zuba hannun jari, da hadin gwiwa, za a iya samar da makoma mai haske ga duniya, mai cike da tsaro da zaman lafiya.

Ya kuma yi nuni da cewa: Yake-yaken da suka gani a duniya sun samo asali ne sakamakon rashin mutunta hakkokin bil’adama da na kasashe, Pezeshkian ya jaddada mutunta yankin kasar Iran da hakkokin kasashe, yana mai bayyana Shirin Iran na gudanar da duk wani hadin gwiwa a fannin kimiyya, tattalin arziki, siyasa, da zamantakewa da duniya, da kuma mika ilimi ga sauran kasashe ba tare da iyakancewa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114