Karin Kudin “Data” A Najeriya Ya Fusata Mutanen Kasar Dake Fama Da Matsananciyar Rayuwa
Published: 13th, February 2025 GMT
Mutanen Najeriya suna bayyana fushinsu akan kara kudaden sayen cajin shiga kafar sadarwa na Internet –Data- da manyan kamfanoni irin su MTN da Airtel su ka yi, saboda yadda ake fama da matsalar rayuwa.
Kamfanin MTN shi ne mafi girma a tsakanin kamfanonin samar da hidimomi na hanyar sadarwa, inda a yanzu ake sayar da Giga 15, akan Naira 6,000 bayan da a baya take naira 2,000 ( wato daga dala 1.
33-3.99) da hakan yake nufin cewa an rubanya farashin sau uku.
Shi ma kamfanin Airtel ya kara yawan kudaden cajin nashi da kaso mai yawa.
Wannan Karin da kamfanonin su ka yi, ya bakanta ran masu amfani da su, musamman a wannan lokacin da ake fama da yanayi mai tsanani na tattalin arziki.
Kamfanin MTN ya wallafa sanarwa a shafinsa na X cewa; Karin kudin ya zama wajibi domin gabatar da hidimomi masu nagarta ga kwastomominsa, tare da neman gafara ga abokan hulda.
Wani daga cikin masu tofa albarkacin baki akan Karin na MNT; ya walllafa cewa; Rubanya kudi har sau uku? Lallai karshen duniya ya zo.”
Ana hasashen cewa Karin da aka yi zai shafi kananan ‘yan kasuwa da suke dogaro da hanyoyin sadarwar masu saukin kudi domin tafiyar da harkokinsu.
Ya zuwa yanzu dai kamfanin Globacom, da shi ne kamfani na uku mafi grima a cikin kasar, bai yi Karin kudin ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
An gudanar da taron tattaunawa na duniya kan kirkire-kirkire da bude kofa da ci gaba na bai daya, jiya Juma’a a birnin Lagos na Nijeriya. Yayin taron wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG da karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos suka shirya, ministan kula da harkokin matasa na Nijeriya Ayodele Olawande da shugaban CMG Shen Haixiong, sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo.
A cewar ministan na Nijeriya, cikin shekaru 5 da suka gabata, dubban matasan kasar sun ci gajiyar tallafin karatu da shirye-shiryen horo da na musaya da Sin ta samar, kuma wannan hadin gwiwa da ake yi a aikace ya kara fahimta da aminci tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, a shirye ma’aikatarsa take ta karfafa hadin gwiwa da sassa masu ruwa da tsaki na kasar Sin wajen ci gaba da fadada shirye-shiryen musaya da na hadin gwiwa da suka shafi matasa.
A nasa bangare, Shen Haixiong ya ce a matsayinta na babbar kafar yada labarai dake watsa shirye shiryenta ga sassa daban daban na duniya, tashar talabijin ta CCTV dake karkashin CMG da abokan huldarta, za su yayata shawarar Sin ta jagorantar harkokin duniya da gabatar da tafarkin Sin na zamanantar da kanta da karfinta na kirkire kirkire a sabon zamani ga al’ummar duniya. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA