HausaTv:
2025-07-31@16:48:58 GMT

Hamas Ta Yi Watsi Da Barazanar Amurka Da Isra’ila Kan Musayar Fursunoni

Published: 13th, February 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi watsi da barazanar da Isra’ila da Amurka ke yi kan batun musayar fursunoni.

Kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem ya fada cewa Isra’ila tana kaucewa aiwatar da wasu tanade-tanade na yarjejeniyar tsagaita bude wuta,” yana mai gargadin cewa ba za a sako mutanen da ake garkuwa da su ba idan ba Isra’ila ta mutunta yarjejeniyar ba.

Qassem ya ce, “Matsayinmu a fili yake, kuma ba za mu amince da barazanar Amurka da Isra’ila ba,” in ji Qassem, bayan firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu ya yi barazanar komwa yaki idan har ba a sako mutanen da aka kama ba zuwa ranar Asabar.

A ranar Laraba, ministan harkokin soji na gwamnatin ya yi gargadin cewa Isra’ila za ta sake fara yakin Gaza idan Hamas ta gaza sakin ‘yan Isra’ila da take tsare da su kuma a wannan karon za ta yi barna.

“Sabon yakin na Gaza zai sha bamban kuma mai tsanani da wanda ya gabata kafin tsagaita bude wuta, kuma ba zai kare ba sai mun fatattaki Hamas da kuma sako dukkan mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji Isra’ila Katz a cikin wata sanarwa.

“Hakan kuma zai ba da damar tabbatar shirin shugaban Amurka Donald Trump game da Gaza,” in ji Katz, yayin da yake magana kan shirin shugaban Amurka na mamaye yankin Falasdinu.

A baya dai kungiyar Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, wata tawaga karkashin jagorancin babban mai shiga tsakani ta isa birnin Alkahira inda ta fara ganawa da jami’an Masar” suna sa ido kan yadda ake aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Ministan ya kuma ce ƙasarsa na shirin sanya hannu a wata takarda don neman goyon bayan sauran ƙasashe wajen ganin an kafa ƙasar Falasɗinu da Isra’ila.

A taron Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar na kwana biyu, ƙasashe 125 sun amince cewa hanyar warware rikicin Gaza ita ce kafa ƙasashe biyu, wato Falasɗinu da Isra’ila.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki