Hamas Ta Yi Watsi Da Barazanar Amurka Da Isra’ila Kan Musayar Fursunoni
Published: 13th, February 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi watsi da barazanar da Isra’ila da Amurka ke yi kan batun musayar fursunoni.
Kakakin kungiyar Hamas Hazem Qassem ya fada cewa Isra’ila tana kaucewa aiwatar da wasu tanade-tanade na yarjejeniyar tsagaita bude wuta,” yana mai gargadin cewa ba za a sako mutanen da ake garkuwa da su ba idan ba Isra’ila ta mutunta yarjejeniyar ba.
Qassem ya ce, “Matsayinmu a fili yake, kuma ba za mu amince da barazanar Amurka da Isra’ila ba,” in ji Qassem, bayan firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu ya yi barazanar komwa yaki idan har ba a sako mutanen da aka kama ba zuwa ranar Asabar.
A ranar Laraba, ministan harkokin soji na gwamnatin ya yi gargadin cewa Isra’ila za ta sake fara yakin Gaza idan Hamas ta gaza sakin ‘yan Isra’ila da take tsare da su kuma a wannan karon za ta yi barna.
“Sabon yakin na Gaza zai sha bamban kuma mai tsanani da wanda ya gabata kafin tsagaita bude wuta, kuma ba zai kare ba sai mun fatattaki Hamas da kuma sako dukkan mutanen da aka yi garkuwa da su,” in ji Isra’ila Katz a cikin wata sanarwa.
“Hakan kuma zai ba da damar tabbatar shirin shugaban Amurka Donald Trump game da Gaza,” in ji Katz, yayin da yake magana kan shirin shugaban Amurka na mamaye yankin Falasdinu.
A baya dai kungiyar Hamas ta bayyana a cikin wata sanarwa cewa, wata tawaga karkashin jagorancin babban mai shiga tsakani ta isa birnin Alkahira inda ta fara ganawa da jami’an Masar” suna sa ido kan yadda ake aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
Kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO, ta gudanar da taron shekara-shekara na biyu, na hukumar zartaswar cinikayyar hidimomi a birnin Geneva dake kasar Switzerland a jiya Juma’a, inda bangaren Sin ya yi nuni da cewa, matakin Amurka game da harajin kwastam na tattare da rashin fahimta da rashin gaskiya a wasu fannoni, don haka ya bukaci bangaren Amurka da ta bi ka’idojin kungiyar WTO, da daidaita matsaloli ta hanyar yin hadin gwiwa a tsakanin bangarori daban daban, da dakatar da daukar matakai daga bangare daya, don tabbatar da tsarin ciniki na duniya tare da bangarori daban daban. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp