An Yi Bikin Cika Shekaru 46 Da Samun Nasarar Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran A Nijar
Published: 9th, February 2025 GMT
A Nijar an yi bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran a Yamai babban birnin kasar, bikin da ya samu halartar ‘yan siyasa da jakadu da jami’an diflomasiyya da ‘yan jarida.
Manyan baki da suka halarci bikin sun hada da ministan harkokin wajen Nijar, magajin garin Yamai da kuma wakili na musamman na Firaministan Nijar.
A yayin wannan biki, jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Nijar Ali Tiztak ya gabatar da jawabi, inda ya yi ishara da irin nasarorin da Tehran ta samu cikin shekaru arba’in da suka gabata.
Ali Tiztak ya ci gaba da cewa, duk da takunkumin zalinci da kalubalen da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take fuskanta tun ranar farko bayan nasarar juyin juya halin Musulunci, ta samu ci gaba da dama a fannonin kiwon lafiya da jiyya, ilimi, kimiyya da fasaha, hakkin dan Adam, tsaro da tsaro.
A wani bangare na jawabin nasa, ya yi ishara da muhimman batutuwan da suka shafi manufofin ketare na kasar Iran, wato tabbatar da moriyar kasar, kiyaye tsaron kasa, tabbatar da daidaiton alaka da dukkanin al’ummomi bisa tushen tattaunawa, daidaito da mutunta juna, raya diflomasiyya da tattalin arziki da kuma mutunta ‘yancin kai da yankunan kasashen.
Yayin da yake ishara da alakar da ke tsakanin Tehran da Yamai, jakadan Iran a Jamhuriyar Nijar ya bayyana aniyar manyan jami’an kasashen biyu na fadada hadin gwiwarsu a fannonin siyasa, tattalin arziki, al’adu da kuma jin kai.
Bugu da kari, Ali Tiztak ya yaba da kokarin gwamnati da al’ummar Nijar a cikin shekara daya da rabi na tabbatar da ‘yancin kansu, ta fuskar tattalin arziki, tsaro da zaman lafiyar al’umma.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta hana yunqurin fasa wani shago da wasu vata-gari suka yi qoqarin yi a Unguwar Buba Shongo da ke cikin birnin Gombe, inda ta qwato wani babur da kayan da ake zargin an yi niyyar amfani da su wajen fasa shagon.
A cewar sanarwar da mai Magana da Yawun Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, lamarin ya faru ne da misalin qarfe 3:00 na safiyar Litinin, 1 ga Watan Yuli, 2025, lokacin da jami’an Operation Hattara ke kan sintiri a daren.
Jami’an sun hango wasu mutane da ba a san ko su wane ne ba suna qoqarin fasa wani shago mallakin wani Muhammadu Adamu Musa, mai shekara 42 da haihuwa.
Da vatagarin suka hango motar sintirin ‘yan sanda na qaratowa, sai suka tsere suka bar shagon ba tare da cimma burinsu ba.
Kayan da aka samu a wurin sun haxa da baqin babur qirar Yamaha mai lamba GME 480 VN da wani qarfe na tanqwara qoafa da takalmin roba guda xaya.
“Dukkan kayan da aka qwato suna hannun ‘yan sanda, kuma bincike yana ci gaba a kan zargin haxa baki da yunqurin aikata laifi,” in ji sanarwar.
Rundunar ta bayyana cewa wannan lamari ya qara tabbatar da cewar dokar da ta takaita zirga-zirgar babura a cikin dare a faxin jihar na nan daram, domin yawan laifukan da ake aikatawa da su a wannan lokaci na dare.
Rundunar ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa tana ci gaba da qoqari don kamo waxanda suka gudu tare da gurfanar da su a gaban shari’a.
Haka zalika, rundunar ta buqaci jama’a da su kasance masu lura da abin da ke faruwa a muhallansu tare da ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma