An Yi Bikin Cika Shekaru 46 Da Samun Nasarar Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran A Nijar
Published: 9th, February 2025 GMT
A Nijar an yi bikin cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a Iran a Yamai babban birnin kasar, bikin da ya samu halartar ‘yan siyasa da jakadu da jami’an diflomasiyya da ‘yan jarida.
Manyan baki da suka halarci bikin sun hada da ministan harkokin wajen Nijar, magajin garin Yamai da kuma wakili na musamman na Firaministan Nijar.
A yayin wannan biki, jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Nijar Ali Tiztak ya gabatar da jawabi, inda ya yi ishara da irin nasarorin da Tehran ta samu cikin shekaru arba’in da suka gabata.
Ali Tiztak ya ci gaba da cewa, duk da takunkumin zalinci da kalubalen da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take fuskanta tun ranar farko bayan nasarar juyin juya halin Musulunci, ta samu ci gaba da dama a fannonin kiwon lafiya da jiyya, ilimi, kimiyya da fasaha, hakkin dan Adam, tsaro da tsaro.
A wani bangare na jawabin nasa, ya yi ishara da muhimman batutuwan da suka shafi manufofin ketare na kasar Iran, wato tabbatar da moriyar kasar, kiyaye tsaron kasa, tabbatar da daidaiton alaka da dukkanin al’ummomi bisa tushen tattaunawa, daidaito da mutunta juna, raya diflomasiyya da tattalin arziki da kuma mutunta ‘yancin kai da yankunan kasashen.
Yayin da yake ishara da alakar da ke tsakanin Tehran da Yamai, jakadan Iran a Jamhuriyar Nijar ya bayyana aniyar manyan jami’an kasashen biyu na fadada hadin gwiwarsu a fannonin siyasa, tattalin arziki, al’adu da kuma jin kai.
Bugu da kari, Ali Tiztak ya yaba da kokarin gwamnati da al’ummar Nijar a cikin shekara daya da rabi na tabbatar da ‘yancin kansu, ta fuskar tattalin arziki, tsaro da zaman lafiyar al’umma.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana damuwarsa kan kalaman da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi game da Najeriya.
Kwankwaso, ya yi wannan magana ne bayan Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi game da zargin kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci.
Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da AmurkaA cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso, ya ce Najeriya ƙasa ce mai cikakken ’yanci, wadda ke fama da matsalar tsaro daga miyagu a sassa daban-daban na ƙasar.
“Matsalar tsaron da muke fuskanta ba ta bambanta tsakanin addini, ƙabila ko ra’ayin siyasa,” in ji shi.
Ya buƙaci gwamnatin Amurka da ta tallafa wa Najeriya da sabbin fasahohi domin yaƙar matsalar tsaro maimakon yin kalaman da za su iya raba kan ’yan ƙasa.
“Amurka ya kamata ta taimaka wa hukumomin Najeriya da ingantattun fasahohi don magance matsalolin tsaro, maimakon yin barazanar da za ta ƙara raba ƙasar,” in ji Kwankwaso.
Haka kuma, ya shawarci Gwamnatin Najeriya da ta naɗa jakadu na musamman domin inganta hulɗar diflomasiyya da Amurka da kare muradun ƙasar a matakin duniya.
Ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su zauna lafiya, inda ya bayyana cewa wannan lokaci ne da ya dace a fifita haɗin kan ƙasa ba abin da ke raba ta ba.
“Wannan lokaci ne da ya kamata mu mayar da hankali kan abin da zai haɗa kanmu ba wanda zai raba mu ba. Allah Ya albarkaci Najeriya,” in ji shi.