Leadership News Hausa:
2025-06-15@09:54:23 GMT

Akwai Arzikin Duniya Da Na Lahira A Harkar Fim- Malam Inuwa

Published: 9th, February 2025 GMT

Akwai Arzikin Duniya Da Na Lahira A Harkar Fim- Malam Inuwa

A zamanin baya, duk da cewa fina-finan nanaye sun fi karbuwa a wajen mutane, amma haka muke kokartawa wajen ganin an shigar da wata koyarwa ta addinin musulinci ko kuma wani abu mai amfani da zai amfanar da al’umma ta wani bangare, amma yanzu duk an daina wannan, masu shirya fina-finai na amfani da labarai masu tsafta da amfanarwa, ba tare da da sanya wakoki ko makamantansu a ciki ba, in ji Malam.

“Dalili kuwa shi ne, yanzu ‘ya’yan mutunci da arziki su ne ke yin harkar, sannan kuma su ne suke samun arzikin duniya da na lahira, akwai lokacin da har mata masu zaman kansu din, sai da muka daina samun su idan zamu yi fim, amma yanzu wannan duk ya zama tarihi”, in ji shi.

Game da tambayar da aka yi masa a kan yadda mutane ke kallon sa, duba da cewa; shi malami ne na addinin musulinci, kuma jarumi a Masana’antar Kannywood cewa ya yi, mutane na yi masa kallon wani Waliyyi a cikinsu, duba da yadda yake isar da sako ko warware wasu matsaloli na musulunci da suka shige wa al’umma duhu ta hanyar fim.

Dangane da yadda yake kallon tarbiyar jaruman Kannywood na yanzu maza da mata, Malam ya sake jaddada maganarsa ta cewa; mutanen kirki ne matuka, sannan akwai wasu maganganu da wasu jahilai wadanda ake yi wa kallon malamai suke yi dangane da jaruman wannan masana’anta ta Kannywood, domin idan har wani zai yanke hukunci a kan tarbiyar jaruman Kannywood, to ba zai wuce mu da muke tare da su ba.

Sannan kuma, duk duniya babu wani jarumin fim mutumin kirki irin dan Masana’antar Kannywood, domin kuwa shi kadai ne yake yin fina-finansa da sauran al’amuran rayuwa a gaban jama’a kowa yana gani, ba tare da ya saka wani hijabi ba, sannan dan Kannywood; ba ya ashariya, ba a hada jiki tsakanin mace da namij, ballantana har ta kai ga sumbata kamar yadda muke gani ana yi a wasu masana’antun shirya fina-finai a sauran sassan duniya.

Daga karshe, ya bayyana cewa; dukkannin wani malami da ma wanda ba malami ba, ya sani duk lokacin da ka bayyana wani abu marar kyawu da wani ya yi a boye ko da yana yi, amma sai ya boye yayin da zai aikata wannan abu, to ka sani Manzon Allah SAW ya ce, ba za ka mutu ba sai ka aikata wannan abu da ka ce yana yi, ko da kuwa yana yi din.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri

A wani bayani na hadin gwiwa da hukumar makamashin Nukiliya ta Iran da kuma ma’aikatar harkokin wajen Iran su ka fitar, sun bayar da umarnin a bude wani wuri na daban na sirri domin ci gaba da tace sanadarin Urani’um, sannan kuma a maye gurbin bututu tace sanadarin mai  mataki na daya, da mai mataki na shida a cibiyar “Pardo.”

Bayanin dai ya zo ne a matsayin mayar da martani ga sanarwar da ta fito daga kwamitin alkalai na hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa akan Iran.

Bugu da kari, bayanin na Iran ya kuma ce; A kodayaushe jamhuriyar musulunci ta Iran tana aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta, kuma har ya zuwa yanzu babu wani rahoto na hukumar wanda ya bayyana cewa; Iran ba ta aiki da ka’idojin hana yaduwar makaman Nukiliya.”

Haka nan kuma bayanin ya ambaci cewa; Tare da cewa Iran tana daukar rahoton da cewa na siyasa ne, wanda Amurka da kasashen turai suke amfani da hukumar a matsayin makami, ba tare da dogaro da wani dalili na ilimi ba.

Har ila yau Iran din ta zargi Amurka da kasashen na turai da wuce gona da iri wajen tsara rahoton da yake cin karo da rahoton da shugaban hukumar ta makamashin Nukiliya ya fitar, wanda bai sami wani abu mai  shiga duhu ba a cikin Shirin na Iran na zama lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • MDD: Adadin ‘Yan Gudun Hijira A Duniya Ya Kai Miliyan 122