Leadership News Hausa:
2025-07-31@02:47:38 GMT

Akwai Arzikin Duniya Da Na Lahira A Harkar Fim- Malam Inuwa

Published: 9th, February 2025 GMT

Akwai Arzikin Duniya Da Na Lahira A Harkar Fim- Malam Inuwa

A zamanin baya, duk da cewa fina-finan nanaye sun fi karbuwa a wajen mutane, amma haka muke kokartawa wajen ganin an shigar da wata koyarwa ta addinin musulinci ko kuma wani abu mai amfani da zai amfanar da al’umma ta wani bangare, amma yanzu duk an daina wannan, masu shirya fina-finai na amfani da labarai masu tsafta da amfanarwa, ba tare da da sanya wakoki ko makamantansu a ciki ba, in ji Malam.

“Dalili kuwa shi ne, yanzu ‘ya’yan mutunci da arziki su ne ke yin harkar, sannan kuma su ne suke samun arzikin duniya da na lahira, akwai lokacin da har mata masu zaman kansu din, sai da muka daina samun su idan zamu yi fim, amma yanzu wannan duk ya zama tarihi”, in ji shi.

Game da tambayar da aka yi masa a kan yadda mutane ke kallon sa, duba da cewa; shi malami ne na addinin musulinci, kuma jarumi a Masana’antar Kannywood cewa ya yi, mutane na yi masa kallon wani Waliyyi a cikinsu, duba da yadda yake isar da sako ko warware wasu matsaloli na musulunci da suka shige wa al’umma duhu ta hanyar fim.

Dangane da yadda yake kallon tarbiyar jaruman Kannywood na yanzu maza da mata, Malam ya sake jaddada maganarsa ta cewa; mutanen kirki ne matuka, sannan akwai wasu maganganu da wasu jahilai wadanda ake yi wa kallon malamai suke yi dangane da jaruman wannan masana’anta ta Kannywood, domin idan har wani zai yanke hukunci a kan tarbiyar jaruman Kannywood, to ba zai wuce mu da muke tare da su ba.

Sannan kuma, duk duniya babu wani jarumin fim mutumin kirki irin dan Masana’antar Kannywood, domin kuwa shi kadai ne yake yin fina-finansa da sauran al’amuran rayuwa a gaban jama’a kowa yana gani, ba tare da ya saka wani hijabi ba, sannan dan Kannywood; ba ya ashariya, ba a hada jiki tsakanin mace da namij, ballantana har ta kai ga sumbata kamar yadda muke gani ana yi a wasu masana’antun shirya fina-finai a sauran sassan duniya.

Daga karshe, ya bayyana cewa; dukkannin wani malami da ma wanda ba malami ba, ya sani duk lokacin da ka bayyana wani abu marar kyawu da wani ya yi a boye ko da yana yi, amma sai ya boye yayin da zai aikata wannan abu, to ka sani Manzon Allah SAW ya ce, ba za ka mutu ba sai ka aikata wannan abu da ka ce yana yi, ko da kuwa yana yi din.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da aniyar ta ta bunƙasa harkar kiwon dabbobi a Nijeriya a matsayin wata muhimmiyar hanya ta magance rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, tare da amfani da damar tattalin arzikin da ke cikin ɓangaren.

Ɗaya daga cikin Shugabannin Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Harkar Kiwo, Farfesa Attahiru Jega, shi ne ya bayyana hakan a wurin taron tattaunawa tsakanin gwamnati da ‘yan ƙasa, wanda Gidauniyar Sa Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna, a ranar Laraba.

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

Jega ya bayyana cewa sabuwar Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo tana ɗaya daga cikin ginshiƙan da ke cikin shirin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na sauya fasalin ɓangaren kiwon dabbobi.

Ya jaddada cewa ana aiwatar da hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba tare da son rai na siyasa ba, tare da mayar da hankali kan haɗa kai da duk masu ruwa da tsaki, ciki har da gwamnatocin jihohi, sarakunan gargajiya, al’ummomin makiyaya da sauran muhimman masu ruwa da tsaki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya