An Yi Zanga-zangar Adawa Da Shirin Trump Na Korar Falasdinawa Daga Gaza
Published: 8th, February 2025 GMT
Dubban masu zanga-zanga ne suka fito kan titunan kasar Jordan da kasar Iraki domin yin Allah wadai da shirin shugaban Amurka Donald Trump na korar Falasdinawa daga yankin Gaza.
Masu zanga-zanga a Amman babban birnin kasar Jordan, da kuma wasu garuruwan kasar Larabawa, sun yi zanga-zangar nuna adawa da shirin na tilastawa mazauna zirin Gaza kaura.
A Jodan an gabatar da wani sabon daftarin doka a majalisar dokokin kasar da zai haramta tilastawa Falasdinawa komawa Jordan.
An kuma gudanar da zanga-zangar adawa da shirin a Bagadaza babban birnin kasar Iraki, baya ga Masar inda aka yi irin wannan zanga-zangar.
Yayin ganawarsa da firayi ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a ranar Alhamis, Trump ya bayyana shirinsa na kwace yankin Gaza na Falasdinu tare da korarsu daga yankin inda ya bukaci kasashen Masar da Jordan dasu karbe su duk da cewa kasashen biyu sun yi watsi da shirin a hukumance.
Shirin na Trump, ya ci karo da tofin Allah tsine daga shugabannin kasashen duniya da dama da kuma babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya yi karin haske game da taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarta a Kazakhstan, yana mai cewa, Sin na da yakininta hanyar taro, ita da sauran kasashen yankin tsakiyar Asiya biyar, za su zurfafa dunkulewa, da amincewa da juna, da gina matsaya guda ta fuskar hadin gwiwa, da zurfafa daidaiton dabarun ci gaba, da daga matsayin hadin gwiwarsu a fannoni daban daban, da kara kuzarin gina al’umma mai makomar bai daya ta Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya.
Bisa gayyatar da shugaban jamhuriyar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya yi masa, shugaba Xi Jinping zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, tsakanin ranekun 16 zuwa 18 ga watan nan na Yuni. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp