Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-01@04:47:30 GMT

An Kammala Taron Bitar Dabarun Yaki Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

Published: 7th, February 2025 GMT

An Kammala Taron Bitar Dabarun Yaki Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

Rundunar sojin Najeriya ta ce tana aiki kan hanyoyin da za su yaki ‘yan bindiga da sauran masu tada kayar baya ta hanyar amfani da darussan da aka koya a wajen wani bada horo da ya gudana a Sakkwato.

 

Babban Hafsan Sojojin Najeriya Laftanar Janar Olufemi Oluyede ya bayyana haka a Sokoto a wajen wani taron karawa juna sani da nufin tattauna sabbin dabarun murkushe ‘yan bindiga da sauran ayyukan tada kayar baya a yankin Arewa maso Yamma, wanda aka gudanar a Runduna ta 8 ta Sojojin Najeriya dake Sokoto.

 

Wanda ya samu wakilcin babban hafsa Manjo Janar Olusegun Samson Abai, ya ce ziyarar wayar da kan ta taso ne domin inganta aikin da ake yi ta hanyar amfani da darasin da aka koyo na sojojin Najeriya.

 

Ya jaddada cewa taron karawa juna sani na daya daga cikin matakai da dama da aka dauka domin dakile kalubalen da sojojin ke fuskanta a yayin da suke gudanar da ayyukansu cikin yanayi mai sarkakiya da rashin tabbas.

 

Babban hafsan sojin kasa Laftanar Janar Olufemi, Oluyede, ya ci gaba da cewa, sojojin Najeriya na ci gaba da duba dabarunsu da hanyoyin da suke bi domin fito da dabarun shawo kan wannan kalubale.

 

Ya lura cewa dole ne kwamandoji a kowane mataki su ci gaba da samar da sabbin dabaru don inganta hanyoyinsu.

 

Ya bayyana cewa matakin ya yi daidai da Falsafar sa a wani yunkuri na karfafa sauye-sauyen da sojojin Najeriya ke yi domin ba da darasin da ya dace da kuma shirin rundunar na sauke nauyin da kundin tsarin mulki ya tanada a cikin hadin gwiwa da hukumomi da dama.

 

Rediyon Najeriya dake Sokoto ya rawaito cewa an shirya taron karawa juna sani ga kananan hafsoshi da matsakaitan shugabannin sojojin Najeriya.

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sakkwato Taro sojojin Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, ɗaya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan ƙasar.

Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi — shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ke iya haifarwa a rayuwar talaka?

NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki” DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

A kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Sabbin Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci: Nan Ba Da Jimawa Ba, ‘Yan Ta’adda Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu – COAS
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi