Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-18@08:17:58 GMT

An Kammala Taron Bitar Dabarun Yaki Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

Published: 7th, February 2025 GMT

An Kammala Taron Bitar Dabarun Yaki Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

Rundunar sojin Najeriya ta ce tana aiki kan hanyoyin da za su yaki ‘yan bindiga da sauran masu tada kayar baya ta hanyar amfani da darussan da aka koya a wajen wani bada horo da ya gudana a Sakkwato.

 

Babban Hafsan Sojojin Najeriya Laftanar Janar Olufemi Oluyede ya bayyana haka a Sokoto a wajen wani taron karawa juna sani da nufin tattauna sabbin dabarun murkushe ‘yan bindiga da sauran ayyukan tada kayar baya a yankin Arewa maso Yamma, wanda aka gudanar a Runduna ta 8 ta Sojojin Najeriya dake Sokoto.

 

Wanda ya samu wakilcin babban hafsa Manjo Janar Olusegun Samson Abai, ya ce ziyarar wayar da kan ta taso ne domin inganta aikin da ake yi ta hanyar amfani da darasin da aka koyo na sojojin Najeriya.

 

Ya jaddada cewa taron karawa juna sani na daya daga cikin matakai da dama da aka dauka domin dakile kalubalen da sojojin ke fuskanta a yayin da suke gudanar da ayyukansu cikin yanayi mai sarkakiya da rashin tabbas.

 

Babban hafsan sojin kasa Laftanar Janar Olufemi, Oluyede, ya ci gaba da cewa, sojojin Najeriya na ci gaba da duba dabarunsu da hanyoyin da suke bi domin fito da dabarun shawo kan wannan kalubale.

 

Ya lura cewa dole ne kwamandoji a kowane mataki su ci gaba da samar da sabbin dabaru don inganta hanyoyinsu.

 

Ya bayyana cewa matakin ya yi daidai da Falsafar sa a wani yunkuri na karfafa sauye-sauyen da sojojin Najeriya ke yi domin ba da darasin da ya dace da kuma shirin rundunar na sauke nauyin da kundin tsarin mulki ya tanada a cikin hadin gwiwa da hukumomi da dama.

 

Rediyon Najeriya dake Sokoto ya rawaito cewa an shirya taron karawa juna sani ga kananan hafsoshi da matsakaitan shugabannin sojojin Najeriya.

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sakkwato Taro sojojin Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

 

Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta