Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-01@06:58:37 GMT

An Kammala Taron Bitar Dabarun Yaki Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

Published: 7th, February 2025 GMT

An Kammala Taron Bitar Dabarun Yaki Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

Rundunar sojin Najeriya ta ce tana aiki kan hanyoyin da za su yaki ‘yan bindiga da sauran masu tada kayar baya ta hanyar amfani da darussan da aka koya a wajen wani bada horo da ya gudana a Sakkwato.

 

Babban Hafsan Sojojin Najeriya Laftanar Janar Olufemi Oluyede ya bayyana haka a Sokoto a wajen wani taron karawa juna sani da nufin tattauna sabbin dabarun murkushe ‘yan bindiga da sauran ayyukan tada kayar baya a yankin Arewa maso Yamma, wanda aka gudanar a Runduna ta 8 ta Sojojin Najeriya dake Sokoto.

 

Wanda ya samu wakilcin babban hafsa Manjo Janar Olusegun Samson Abai, ya ce ziyarar wayar da kan ta taso ne domin inganta aikin da ake yi ta hanyar amfani da darasin da aka koyo na sojojin Najeriya.

 

Ya jaddada cewa taron karawa juna sani na daya daga cikin matakai da dama da aka dauka domin dakile kalubalen da sojojin ke fuskanta a yayin da suke gudanar da ayyukansu cikin yanayi mai sarkakiya da rashin tabbas.

 

Babban hafsan sojin kasa Laftanar Janar Olufemi, Oluyede, ya ci gaba da cewa, sojojin Najeriya na ci gaba da duba dabarunsu da hanyoyin da suke bi domin fito da dabarun shawo kan wannan kalubale.

 

Ya lura cewa dole ne kwamandoji a kowane mataki su ci gaba da samar da sabbin dabaru don inganta hanyoyinsu.

 

Ya bayyana cewa matakin ya yi daidai da Falsafar sa a wani yunkuri na karfafa sauye-sauyen da sojojin Najeriya ke yi domin ba da darasin da ya dace da kuma shirin rundunar na sauke nauyin da kundin tsarin mulki ya tanada a cikin hadin gwiwa da hukumomi da dama.

 

Rediyon Najeriya dake Sokoto ya rawaito cewa an shirya taron karawa juna sani ga kananan hafsoshi da matsakaitan shugabannin sojojin Najeriya.

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sakkwato Taro sojojin Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za ta kammala aikin shimfiɗa layin dogo wanda ya taso daga Kaduna zuwa Kano a cikin shekarar 2026 mai zuwa.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a yau Laraba.

Kazalika, takwaransa na sufuri, Sa’idu Ahmed Alkali ya jaddada hakan ne a yayin jawabinsa a wajen wani taron tuntuɓa tsakanin ’yan ƙasa da gwamnati da ke gudana a Jihar Kaduna.

Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

A cewar ministan, lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya hau mulki kashi 15 cikin 10 na aikin kawai aka kammala.

Wata sanarwa da ma’aikatar yaɗa labarai ta fitar ta ambato ministan yana cewa “amma zuwa yanzu an kammala kashi 53 cikin 100.”

A 2024 Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa ta samu rancen kuɗin da za ta kammala aikin daga wani bankin kasuwanci na ƙasar China, abin da ministan ya jaddada a yau ɗin.

Kazalika, ministan ya ce Gwamnatin Tarayyar ta samu duka kuɗin gudanar da aikin gina layin dogo daga birnin Maiduguri na Jihar Borno zuwa garin Aba na Jihar Abiya.

“Layin dogon mai tsawon kilomita 1,443 zai ratsa jihohin Borno, da Yobe, da Gombe, da Bauchi, da Filato, da Kaduna, da Nasarawa, da Binuwai,” in ji sanarwar da kakakin ministan Rabiu Ibrahim ya fitar.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana inda gwamnatin ta samo kudin ba.

Ministan ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta gyara layin dogo na dakon kaya tsakanin Legas zuwa Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Sojojin Sahayoniya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba