Aminiya:
2025-11-03@02:59:17 GMT

Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa

Published: 7th, February 2025 GMT

Bama-bamai da mayakan Boko Haram suka binne sun kashe mutane biyu a hanyarsu ta zuwa kasuwa a Jihar Adamawa.

Kakakin ’yan sanda a jihar Borno, ASP Kenneth Daso, ya ce mutane shida ne a cikin motar a lokacin motar da ta taka bam din a ranar Talatar bayan ta taso daga Karamar Hukumar Hawul ta Borno zuwa Kasuwar Garkida ta jihar Adamawa.

“Ana zargin cewa ’yan Boko Haram ne suka dasa bama-baman, kuma motar da ke jigilar mutanen kauyen zuwa kasuwa a Garkida ta taka ta kuma ta fashe.

“Wani dan shekara 25 ya mutu nan take, amma sauran fasinjojin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani,” inji shi.

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa

Ya ce ’yan sanda tare da sauran jami’an tsaro suna bakin kokarinsu wajen ganin sun kare yankin daga duk wata matsalar tsaro tare da yin kira ga jama’ar yankin da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi.

Sai dai wani da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa wakilinmu cewa al’ummar kauyukan biyu na fuskantar hare-haren ta’addanci ta hanyar bama-bamai da aka dasa da daddare a kan hanyoyin karkara.

Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su kara tura jami’ansu da makamai a yankin, domin hare-haren ta’addanci a Damboa da Chibok da kuma gefen dajin Sambisa na zama abin damuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Boko Haram Garkida kasuwa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.

Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.

Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.

Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen  tsaro.

CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure