Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa
Published: 7th, February 2025 GMT
Bama-bamai da mayakan Boko Haram suka binne sun kashe mutane biyu a hanyarsu ta zuwa kasuwa a Jihar Adamawa.
Kakakin ’yan sanda a jihar Borno, ASP Kenneth Daso, ya ce mutane shida ne a cikin motar a lokacin motar da ta taka bam din a ranar Talatar bayan ta taso daga Karamar Hukumar Hawul ta Borno zuwa Kasuwar Garkida ta jihar Adamawa.
“Ana zargin cewa ’yan Boko Haram ne suka dasa bama-baman, kuma motar da ke jigilar mutanen kauyen zuwa kasuwa a Garkida ta taka ta kuma ta fashe.
“Wani dan shekara 25 ya mutu nan take, amma sauran fasinjojin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani,” inji shi.
Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A KasuwaYa ce ’yan sanda tare da sauran jami’an tsaro suna bakin kokarinsu wajen ganin sun kare yankin daga duk wata matsalar tsaro tare da yin kira ga jama’ar yankin da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi.
Sai dai wani da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa wakilinmu cewa al’ummar kauyukan biyu na fuskantar hare-haren ta’addanci ta hanyar bama-bamai da aka dasa da daddare a kan hanyoyin karkara.
Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su kara tura jami’ansu da makamai a yankin, domin hare-haren ta’addanci a Damboa da Chibok da kuma gefen dajin Sambisa na zama abin damuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Boko Haram Garkida kasuwa Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
SojojinHKI Sun Kashe Akalla Mutane 75 A Gaza A Ranar Jumma’a Kadai
Sojojin HKI sun sabonta hare-hare a ranar Jumma’a kan fararen hula a kan Falasdinawa a Gaza, inda suka kashe akalla mutane 76 ajiya jumma’a kadai sannan wasu dadama suka ji rauni.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Falasdinawa a Gaza na cewa sojojin HKI sun kai hare-hare a kan wani gida a Khan Yunus inda suka kashe akalla mutane. A wani harin da sojojin yahudawan suka kai khan yunus har’ila yau ya kashe falasdinawa akalla 8.
Alaa Al-Najjar, likita a asbitin Nasir ya bayyana cewa ta rasa yayanta har 9 a cikin asbitin sanadiyyar hare-haren HKI a kan shi.
Harin da yahudawan suka kai kan gidan Annajjar dai ya rusa gidan daga sama har kasa sannan wutan da ya taso daga gidan sai da ya watsu zuwa gidajen da suke makobtaka da gidan nata.
Dr Annajjar ta sami labarin hari a kan gidanta ne a lokacinda take aiki a kan wasu kananan yara. Yayanta sun kama daga shekara 2-16. Sannan mijinta na daga cikin wadanda suka ji rauni.