Aminiya:
2025-07-09@07:48:33 GMT

Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa

Published: 7th, February 2025 GMT

Bama-bamai da mayakan Boko Haram suka binne sun kashe mutane biyu a hanyarsu ta zuwa kasuwa a Jihar Adamawa.

Kakakin ’yan sanda a jihar Borno, ASP Kenneth Daso, ya ce mutane shida ne a cikin motar a lokacin motar da ta taka bam din a ranar Talatar bayan ta taso daga Karamar Hukumar Hawul ta Borno zuwa Kasuwar Garkida ta jihar Adamawa.

“Ana zargin cewa ’yan Boko Haram ne suka dasa bama-baman, kuma motar da ke jigilar mutanen kauyen zuwa kasuwa a Garkida ta taka ta kuma ta fashe.

“Wani dan shekara 25 ya mutu nan take, amma sauran fasinjojin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani,” inji shi.

Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa

Ya ce ’yan sanda tare da sauran jami’an tsaro suna bakin kokarinsu wajen ganin sun kare yankin daga duk wata matsalar tsaro tare da yin kira ga jama’ar yankin da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi.

Sai dai wani da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa wakilinmu cewa al’ummar kauyukan biyu na fuskantar hare-haren ta’addanci ta hanyar bama-bamai da aka dasa da daddare a kan hanyoyin karkara.

Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su kara tura jami’ansu da makamai a yankin, domin hare-haren ta’addanci a Damboa da Chibok da kuma gefen dajin Sambisa na zama abin damuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Boko Haram Garkida kasuwa Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Wata bas kirar Macarpollo dauke da mutane da yi hatsari a Jos

Wata babbas bas din haya kirar Macarpollo dauke da fasinjoji  ta yi hatsari a garin Jos, hedikwatar Filato.

Motar mai daukar fasinjoji 56 ta yi hatsari ne bayan isowarta Mahadar Vom da Anguldi da ke Jos, daga Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas.

Hatsarin ya auku ne kimanin milomita 10 kafin motar ta isa inda za ta tsaya bayan doguwar tafiyar mai nisan kilomita.

Wakilinmu ya gano cewa hatsarin ya auku ne da misalin karfe 4 na asubahin ranar Litinin din nan, inda motar ta lalata kusan daukacin shagunan da ke wurin da ta yi hatsari.

Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da faruwar lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, sun Jikkata 4 a Borno
  • Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China
  • Wata bas kirar Macarpollo dauke da mutane da yi hatsari a Jos
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno
  • Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
  • An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
  • Malamin Addinin Musulunci Yayi Kira Da Ayi Gaggawa Gyaran Hanyar Zamfara
  • Miliyoyin Mutane Sun Yi Juyayin Imam Husain ( a.s) A Karbala
  • Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos