Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-01@06:52:25 GMT

Sojojin Kenya 100 sun isa Haiti domin yaƙi da ƴandaba

Published: 7th, February 2025 GMT

Sojojin Kenya 100 sun isa Haiti domin yaƙi da ƴandaba

Sama da sojojin Kenya 100 ne suka isa ƙasar Haiti, domin karfafa jami’an tsaron Haiti da kuma aikin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, a yaƙin da suke yi da gungun ƴandaba da suka addabi ƙasar.

Sai dai ana nuna damuwa kan yadda har yanzu dakarun suka gaza tabbatar da doka a babban birnin ƙasar, Porto Prince.

An yi ta raɗe-raɗin ayyukan dakarun sun zo ƙarshe, amma kwamandan rundunar, Godfrey Otunge ya ce lamarin ba haka yake ba.

Ya ce lokacin da yake magana da jakadun yana yi ne domin kawar da shakkun da ake yi na aikinsu, ya kuma shaida cewa ƙawancen na nan daram.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kenya

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya

Birtaniya ta sanar da cewa muddin Isra’ila ba ta biyayya wa wasu sharuɗa ba, to kuwa a watan Satumba mai zuwa za ta amince da Falasɗinu a matsayin halastacciyar ƙasa a yayin taron Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA).

Firaiministan Birtaniya Keir Starmer ne ya bayyana haka a wani jawabi da ya gudanar a yau Talata.

Starmer ya ce za su amince da ‘yancin Falasɗinu idan har Isra’ila ba ta ɗauki hanyar kawo ƙarshen halin da ake ciki a Gaza ba, ciki har da tsagaita wuta da kuma tsarin samar da zaman lafiya na din-din-din.

Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya

A cewarsa, hakan zai tabbata “har sai idan Isra’ila ta ɗauki matakai na kawo karshen abin da ke faruwa a Gaza, ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta, ta kuma tabbatar da cewa ba za a ƙwace Gaɓar Yamma ba, har ma da cimma yarjejeniyar zaman lafiya ta tsawon lokaci da za ta haifar da mafitar ƙasashe biyu.”

Firaministan ya ƙara nanata cewa babu wani bambanci tsakanin Isra’ila da Hamas kuma buƙatar da Birtaniya take da su kan Hamas suna nan — cewa dole su saki dukkan waɗanda suke garkuwa da su, su saka hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta, su kuma amince cewa ba za su saka baki a gwamnatin Gaza ba sannan su ajiye makamai.

Starmer ya ce za su ci gaba da duba lamarin da ke faruwa a Gaza gabanin taron babban zauren MDD da za a yi don ganin yadda ɓangarorin biyu suka ɗauki matakai na samar da zaman lafiya kafin ta ɗauki mataki na karshe.

Matakin da Birtaniyar ke shirin dauka na zuwa ne biyo bayan matsin lamba da Starmer ke sha a cikin ƙasar, inda ‘yan majalisu sama da 200 a makon da ya wuce, suka buƙaci ya aminta da ‘yancin Falasɗinu.

Baya ga haka kuma, ɗaruruwan mutane sun gudanar da zanga-zanga a titunan birnin Landan, suna mai kira ga Starmer ya amince da buƙatarsu na a samar da ƙasar Falasɗinu.

Ƙasashe da dama, kusan 139 sun amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa a hukumance, kuma a makon da ya wuce Faransa ta ce za ta yi shelar hakan yayin taron na Majalisar Ɗinkin Duniya da ke gudana yanzu haka.

Rikicin Gabas ta Tsakiya na ƙara ƙamari, inda al’ummar Gaza ke mutuwa a kullum , yayin da suke fuskantar matsananciyar yunwa, abinda wasu ke ganin samar da ƙasar Falasɗinu ne na mafita domin kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya.

A halin yanzu ƙasashen duniya sama da 100 ne ke tattauna makomar Falasdinu a taron Majalisar Ɗinkin Duniya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa matsalar yunwa mafi muni a duniya na shirin faruwa a Gaza, saboda yadda mutane ke mutuwa wasu ke galabaita a dalilin rashin abinci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu