Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya bayyana cewa juyin juya halin musulunci  a nan Iran ya zo ne da sakon zaman lafiya ga dukkan kasashen duniuya, don haka ne ta haramtawa kanta mallakan makaman nukliya wanda yake kissan kare dangi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jiya Alhamis a taron da jakadun kasashen waje da manya-manya baki suka halatta a gidan shugaban kasa a nan Tehran.

Sai dai shugaban ya kara da cewa kissan kananan yara baa bin amincewa ne a garemu,

Sannan ya ce JMI bata amince da samuwar yan ta’adda a ko ina ba, kuma kasar Iran tana daga cikin kasashe wadanda suka fi cutuwa da ayyukan ta’addanci a duniya.

Sannan daga karshen  shugaban ya kammala da cewa tsarin harkokin wajen kasar Iran ya tafi ne a kan abota zaman lafiya da kuma mu’amala da juna cikin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul

Jami’an diblomasiyya na kasashen Iran da kuma na tarayyar Turai 3 wato Faransa da Jamus da kuma burtaniya sun fara tattaunawa gaba da gaba bayan yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka kai mata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta kara da cewa wannan tattaunawar yana da matukar muhimmanci don zasu tattauna kan shirin makamashin nukliyar kasar Iran da kuma dauke mata takunkuman tattalin arzikin da su dora mata saboda shirinta na makamshin nukliya. Har’ila yau ana ganin tattaunawar ta Istambul shi zai fayyace makomar dangantaka tsakanin Iran da tarayyar Turai gaba daya nan gaba.

Labarin ya kara da cewa tarunn yana gudana ne a cikin ofishin jakadancin kasar Iran dake birnin Istambul kuma Majid Takht-ravanci da kuma Kazem Ghariba abadi , mataimakin ministan harkokin wajen kasar ta Iran ne zasu jagoranci tawagar Iran a tattaunawar.

Kuma tattaunawar zasu maida hankali ne kan al-amura guda biyu. Shirin nukliyar kasar Iran da kuma dauke mata takunkuman tattalin arziki wadanda turawan suka dora mata.

Kafin taron dai ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa, matsayin Iran bai sawya ba, dole ne tashe makamashin Nukliya a cikin gida ya zama cikin shirin makamashin nukliya na kasar Iran. Ya kuma ce duk wani kokari na amfani da SnapBack zai fuskanci maida martani mai tsanani ga wadannan kasashe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi Ya Jaddada Cewa; Karfin Kariya Da Makamai Masu Linzamin Iran Ne Suka Tilastawa Makiya Neman Tsagaita Wuta
  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Nuna Sha’awar Ganawa Da Shugaban Kasar Rasha
  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • Faransa Zata Bayyana Amincewa Da Samuwar kasar falasdinu
  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • Iran Tace Tawagar Kwararru Daga Hukumar IAEA Zata Ziyarci Kasar Nan Ba Da Dadewa Ba
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya