Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya bayyana cewa juyin juya halin musulunci  a nan Iran ya zo ne da sakon zaman lafiya ga dukkan kasashen duniuya, don haka ne ta haramtawa kanta mallakan makaman nukliya wanda yake kissan kare dangi.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a jiya Alhamis a taron da jakadun kasashen waje da manya-manya baki suka halatta a gidan shugaban kasa a nan Tehran.

Sai dai shugaban ya kara da cewa kissan kananan yara baa bin amincewa ne a garemu,

Sannan ya ce JMI bata amince da samuwar yan ta’adda a ko ina ba, kuma kasar Iran tana daga cikin kasashe wadanda suka fi cutuwa da ayyukan ta’addanci a duniya.

Sannan daga karshen  shugaban ya kammala da cewa tsarin harkokin wajen kasar Iran ya tafi ne a kan abota zaman lafiya da kuma mu’amala da juna cikin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Lafiyar Sudan Ta Ce: An Dan Samu Ja Da Baya A Cutar Kwalara Da Ta Kunno Kai A Kasar

Ma’aikatar lafiyar kasar Sudan ta bayyana cewa: Ana ci gaba da daukan matakan ganin an shawo kan ci gaba da yaduwar masifar kwalara a kasar

Gidan talabijin na Al-Alam ya watsa rahoton cewa: A halin da ake ciki a fannin kiwon lafiya a birnin Khartoum fadar mulkin kasar bayan bullar cutar kwalara yana ta kokarin ya shawo kan matsalar tare da killace mutanen da suka kamu da cutar a wurare na musamman a babban birnin kasar Khartoum, rahotonni sun bayyana cewa: Cutar ta bazu cikin sauri a birnin. Sannan ma’aikatar lafiya ta Sudan da kungiyoyi da dama suna ci gaba da kokarin shawo kan cutar don kada ta zama annoba wadda za ta yadu zuwa jihohi da dama.

Wakilin gidan talabijin na Al-Alam na kasar Iran ya yi nuni da cewa: Akwai kuma jahohi da dama a yankin Darfur, wadanda wasu daga cikinsu suka kamu da cutar kwalara, inda ya ce daya daga cikin abubuwan da ke kawo wannan cuta shi ne yanayin da ake fama da shi a yankin Al-Salha, inda aka shafe fiye da wata guda ana gwabza fada tsakanin sojojin Sudan da ‘yan tawayen kasar na dakarun kai daukin gaggawa, inda gawarwakin mutane suke kwance a gefen hanya, kuma sun kwashe sama da wata guda, babu wani yunkurin kwashe su, don haka suke wari tare da gurbata yanayi, wasu gawarwakin kuma aka kai su cikin teku. Duk wannan na daya daga cikin dalilan da suka haifar da yaduwar wannan cuta, amma ta dan ja da baya, a cewar ministan lafiya na tarayya, wanda ya zo musamman Khartoum domin fayyace lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
  • Ma’aikatar Lafiyar Sudan Ta Ce: An Dan Samu Ja Da Baya A Cutar Kwalara Da Ta Kunno Kai A Kasar
  • Oman ta mika wa Iran takardun shawararin Amurka game da tattaunawar nukiliya
  • Nijar : Kasashen Faransa da Amurka ne ke kitsa mana hare-haren ta’addanci  
  • Iran Ta Kaddamarda Sabbin Magunguna Har 23 Tare Riga Kafin HPV A Karon Farko A Kasar
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  •  DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23