Aminiya:
2025-05-01@04:17:28 GMT

Ɗan firamare ya je makaranta da bindiga yana barazanar harbe ɗalibai

Published: 6th, February 2025 GMT

An kama wani ɗalibin firamare mai shekara 13 ɗauke da bindiga a makaranta, inda yake barazanar harbe abokan karatunsa da ita.

Bayan nan ne jami’an tsaro suka yi nasarar kama shi a Makarantar Firamare ta St. Paul da ke ƙauyen Ikot Ibiok a Ƙaramar Hukumar Eket a Jihar Akwa Ibom.

A safiyar Alhamis ne kakakin runduanr ’yan sandan jihar, DSP Timfon John, ta sanar da kama yaron.

DSP Timfon John ta bayyana cewa, a yayin bincike sun gano cewa yaron ya shafe kimanin wata uku yana zuwa da bindigar makaranta.

An kashe wa ma’aurata ’ya’yansu uku an ɓoye gawarsu a firinji Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata

Ta bayyana cewa ya shaida musu cewa tun a watan Nuwambar shekarar 2024 ya ɗauko bindigar daga kwabar tufafi da ke ɗakin mahaifinsa yake amfani da ita.

Ta ce bayan samun rahoto ne, “ba tare da ɓata lokaci ba rundunar ta garzaya ta kama yaron tare da ƙwace bindigar hannun, wadda ƙirar gida ce.

“A yayin bincike yaron ya shaida mana cewa tun watan Nuwambar 2024 bindigar take hannunsa, kuna ya dauko ta ne daga kwabar mahaifinsa, wanda shi ma daga bisani muka kama shi, muna bincikar su tare.”

Ɗan shekara 60 ya lalata ’yar shekara 9

Ta ce rundunar ta kuma cika hannu da wani ɗan shekara 60 da ya yi wata yarinya mai shekara tara a duniya fyade.

Ta ce dubun tsohon ta cika ne bayan mahaifiyar yarinyar ta kai ƙara a ofishin ’yan sanda daga ƙauyen Afaha Offiong, da ke yankin Nsit Ibom.

Jami’ar ta bayyana wa ’yan sanda cewa bayan ta aiki ’yar tata ne tsohon ya tare ta ya shigar da ita cikin jeji ya keta matuncinta, inda daga baya ya ba ta Naira 200.

Daga bisani jami’an rundunar suka je suka cika hannu da shi kuma nan gaba za a gurfanar da shi a gaban kotu domin ya girbi abin da ya shuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: firamare Makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje

Shugaban kasar Iran ya nuna murnarsa da yin maraba lalai da masu zuba hannun jari daga kasashen waje a Iran

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana Iran a matsayin dandalin da ta dace wajen zuba hannun jari da gudanar da harkar kasuwanci, yana maraba da masu zuba hannun jari na kasashen waje da ‘yan kasuwa na duniya da su shiga harkokin tattalin arziki da zuba hannun jari a Iran.

A yayin bikin bude baje koli karo na bakwai na baje kolin kayayyakin da Iran ke fitarwa zuwa kasashen ketare (Iran Expo 2025) a safiyar yau Litinin, shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi maraba da baki na kasashen waje da suka halarci wannan baje kolin, yana mai cewa, “Ko da yake ana gabatar musu da wani hoto na daban da ya yi hannun riga da hakikanin Iran da al’ummar kasarta a ketare, amma Iran kasa ce mai karbar baki, kuma al’ummarta masu tausayi da nuna jin kai.”

Yana mai jaddada cewa: Iran wata kafa ce da ta dace da zuba hannun jarin kasuwanci da yawon bude ido na ketare, Pezeshkian ya bayyana cewa da wannan karfin, kuma ta hanyar ciniki, zuba hannun jari, da hadin gwiwa, za a iya samar da makoma mai haske ga duniya, mai cike da tsaro da zaman lafiya.

Ya kuma yi nuni da cewa: Yake-yaken da suka gani a duniya sun samo asali ne sakamakon rashin mutunta hakkokin bil’adama da na kasashe, Pezeshkian ya jaddada mutunta yankin kasar Iran da hakkokin kasashe, yana mai bayyana Shirin Iran na gudanar da duk wani hadin gwiwa a fannin kimiyya, tattalin arziki, siyasa, da zamantakewa da duniya, da kuma mika ilimi ga sauran kasashe ba tare da iyakancewa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi