Ɗan firamare ya je makaranta da bindiga yana barazanar harbe ɗalibai
Published: 6th, February 2025 GMT
An kama wani ɗalibin firamare mai shekara 13 ɗauke da bindiga a makaranta, inda yake barazanar harbe abokan karatunsa da ita.
Bayan nan ne jami’an tsaro suka yi nasarar kama shi a Makarantar Firamare ta St. Paul da ke ƙauyen Ikot Ibiok a Ƙaramar Hukumar Eket a Jihar Akwa Ibom.
A safiyar Alhamis ne kakakin runduanr ’yan sandan jihar, DSP Timfon John, ta sanar da kama yaron.
DSP Timfon John ta bayyana cewa, a yayin bincike sun gano cewa yaron ya shafe kimanin wata uku yana zuwa da bindigar makaranta.
An kashe wa ma’aurata ’ya’yansu uku an ɓoye gawarsu a firinji Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar MataTa bayyana cewa ya shaida musu cewa tun a watan Nuwambar shekarar 2024 ya ɗauko bindigar daga kwabar tufafi da ke ɗakin mahaifinsa yake amfani da ita.
Ta ce bayan samun rahoto ne, “ba tare da ɓata lokaci ba rundunar ta garzaya ta kama yaron tare da ƙwace bindigar hannun, wadda ƙirar gida ce.
“A yayin bincike yaron ya shaida mana cewa tun watan Nuwambar 2024 bindigar take hannunsa, kuna ya dauko ta ne daga kwabar mahaifinsa, wanda shi ma daga bisani muka kama shi, muna bincikar su tare.”
Ɗan shekara 60 ya lalata ’yar shekara 9Ta ce rundunar ta kuma cika hannu da wani ɗan shekara 60 da ya yi wata yarinya mai shekara tara a duniya fyade.
Ta ce dubun tsohon ta cika ne bayan mahaifiyar yarinyar ta kai ƙara a ofishin ’yan sanda daga ƙauyen Afaha Offiong, da ke yankin Nsit Ibom.
Jami’ar ta bayyana wa ’yan sanda cewa bayan ta aiki ’yar tata ne tsohon ya tare ta ya shigar da ita cikin jeji ya keta matuncinta, inda daga baya ya ba ta Naira 200.
Daga bisani jami’an rundunar suka je suka cika hannu da shi kuma nan gaba za a gurfanar da shi a gaban kotu domin ya girbi abin da ya shuka.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bayyana cewa: Babu wata tattaunawa da zata yi da Amurka a halin da take ciki na kare kanta
A yayin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke ci gaba da kai hare-hare kan yankunan kasar Iran, a hukumance Iran ta bayyana rashin yiwuwar ci gaba da zaman tattaunawa da Amurka kan batun shirinta na makamshin nukuliya, tare da dora wa Amurka alhakin abin da ke faruwa kai tsaye.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bayyana cewa: Akwai hadin kai tsakanin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka wajen kai hare-hare kan kasar Iran domin rusa zaman tattaunawar nukiliya da haka ke bayyana kawar da duk wata magana ta hakikanin aniyar Amurka na samar da hanyar warware takaddamar Shirin Iran ta hanyar lumana.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa ci gaba da tattaunawa da Amurka a yayin da ake ci gaba da kai hare-haren wuce gona da iri yana gwada tsarin tattaunawar ba shi da ma’ana. Ya yi kakkausar suka ga matakin da hukumar ta IAEA ta dauka, inda ya yi la’akari da hakan a matsayin wani dalili na halasta cin zarafi a kan cibiyoyin nukiliyar Iran.