Gwamnatin Niger Ta Karbi Yara 21 Da Aka Ceto
Published: 6th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Neja ta karbi yara ashirin da daya da aka kama a kan iyakar Najeriya da jamhuriyar Nijar yayin da ake safarar su zuwa Sudan.
Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Yakubu Garba wanda ya bayyana haka a lokacin da yake karbar yaran a madadin gwamnatin jihar Neja a Minna, ya ce an kama yaran ne a cikin kasashen Kamaru da Mali da Jamhuriyar Nijar da kuma Sudan.
Kwamared Yakubu Garba ya bayyana cewa yaran da aka ceto ‘yan karamar hukumar Magama ne a jihar Neja, amma ya yaba da kokarin gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da kuma hukumar fataucin bil’adama bisa nasarar ceto yaran.
Ya ci gaba da cewa ta’addancin ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya sashe na 34 karamin sashe na 1 da sashe na 13 na kundin tsarin mulkin kasa da ya haramta duk wani nau’in safarar mutane a kasar.
Da yake mayar da martani, daya daga cikin iyayen yaran da aka ceto, Jamilu Usman wanda ya bayyana ‘ya’yansa biyu Umar Jamilu mai shekaru 6 da Maruf Jamilu mai shekaru 5 ya bayyana cewa Malam Abubakar sananne ne a wurinsu wanda ya yi karatu a Jamhuriyar Nijar.
Ya bayyana cewa sun ba wa ‘ya’yansu damar tafiya da Malam Abubakar Jamhuriyar Nijar domin samun ilimin addinin Musulunci, inda ya jaddada cewa shi ne shugaban makarantar firamare ta Tungan Gari da ke karamar hukumar Magama, yana da mata hudu da ‘ya’ya talatin kuma zai ajiye aiki nan da shekaru biyar masu zuwa, shi ne ya sa suka bashi ‘ya’yansu.
Sai dai ya kara da cewa suna biyan dubu 35 ga kowane yaro kowane wata domin su sami damar samun ilimin da ake bukata.
KARSHEN ALIYU LAWA/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
A wata hira tare da gidan talabijin na Arise, Obi ya ce duk da cewa cire tallafin mai yana da muhimmanci, amma ya kamata a aiwatar da wannan tsari cikin tsari.
Ya ce ya amince cewa tallafin mai yana cike da ta’asa da cin hanci wanda akwai bukatar a kawo karshensa, amma ya yi suka ga hanyoyin da gwamnatin Tinubu take bi, yana bayyana su a matsayin wadanda aka yi ba bisa kwarewa ba.
Obi ya tambayi jagororin kula da kudin da aka ajiye daga cire tallafin, yana cewa, “Tun da aka ce manatallafin man fetur, ana cewa an cire ne saboda ba a so mu dunga ciyo bashi kuma kudaden za su ba da dama wajen zuba jari a muhimman ababen more rayuwa.
‘’Ina biliyoyin kudaden da aka tara? Ina aka zuba su a muhimman yankunan ci gaba? Kowa na sane da muhimman yankunan ci gaba da suka hada da ilimi, lafiya, da fitar da mutane daga talauci. Shin ko daya daga cikin wadannan abubuwan gda uku ya inganta? A’a.’’
Obi ya ce ya kamata a yi musayar farashi mai da masu ruwa da tsaki da kyau ta yadda zai rage tasirin ga matsalolin da ‘yan kasa ke ciki.
Da yake mayar da martini ga Obi, mai taimaka wa shugaban kasa kan batutuwan tsare-tsare, Daniel Bwala, ya bayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a matsayin mutum mai son kansa wanda ba ya da ilimin warware al’amuran da suka shafi tattalin arziki da shugabanci.
Bwala, a cikin wata sanarwa da ya wallafa ta shafinsa na sada zumunta na Tuwita, ya bayyana cewa ya yi mamakin yadda Obi ya yarda da manufofin tattalin arzikin Shugaba Tinubu, musamman kan cire tallafin mai da hada-hadar kudaden waje, amma ya jaddada cewa Obi sauran manyan ‘yan adawa suna neman samun iko ne kawai ko ta wani hali a wannan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp