Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a zaman lafiya da hakuri a tsakanin al’ummar garin Rimin Zakara sakamakon rikicin filaye da ya barke tsakanin al’umma da Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).

 

Sarkin ya yi wannan roko ne a ziyarar da ya kai yankin bayan dawowarsa daga aikin hajji.

 

Da yake jawabi ga al’ummar yankin, Sarkin ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a rikicin tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka jikkata cikin gaggawa.

 

“Dole ne mu yi wa wadanda suka rasu addu’a da kuma baiwa iyalansu ikon jure wannan rashi, Allah ya sa wannan ya zama na karshe a cikin irin wannan mummunan lamari a cikin al’ummarmu,” inji shi.

 

Sarkin ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu kamun kai tare da ba da damar bin doka da oda, yana mai jaddada cewa tashin hankali yana haifar da karin wahala ne kawai.

 

“Lokacin da tashin hankali ya barke mutanenmu ne ke shan wahala, babu wani barna ko zubar da jini da zai magance matsalar, dole ne mu hada kai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma,” in ji shi.

 

Da yake la’akari da sarkakiyar rigimar da aka kwashe shekaru ana yi, Sarkin ya bayyana cewa al’umma da jami’a suna da’awar mallakar fili a bisa doka. Ya jaddada bukatar a samar da shawarwari ta hanyar kotu da kuma tattaunawa tare da hukumomin da abin ya shafa.

 

“Bai kamata wannan al’amari ya kasance mai sarkakiya ba, idan har shari’ar ta kasance a gaban kotu, dole ne a warware ta da kwararan hujjoji, dole ne mu zauna da dukkan bangarorin da abin ya shafa domin samun maslaha mai dorewa,” inji shi.

 

Domin samar da zaman lafiya, Sarkin ya bayyana shirin kafa wani kwamiti da zai kunshi wakilai daga dukkan masu ruwa da tsaki, da suka hada da gwamnatin jihar, da hukumomin BUK, da hukumomin tsaro, da shugabannin al’umma, domin magance matsalar.

 

“Za mu hada hannu da Gwamna, da hukumomin BUK, da jami’an tsaro don tabbatar da an yi adalci, amma idan kun sayar da filayen ku, kun karbi diyya, to ku amince da gaskiyar lamarin,” in ji shi.

 

Sarkin ya kammala ziyarar tasa inda ya bukaci mazauna yankin da su baiwa zaman lafiya da hadin kai fifiko, yana mai jaddada cewa babu wata kasa ko dukiya da ta kai asarar rayukan bil’adama.

 

“Rayuwar mutum daya ta fi duk duniya daraja, dole ne mu hada kai don ganin ba a sake samun irin wannan bala’i ba, adalci zai yi nasara, kuma Allah yana tare da masu tsayawa kan gaskiya.”

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarki

এছাড়াও পড়ুন:

Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar

Jagoran ‘yan hamayyar siyasar kasar Kamaru Issa Chiroma Bakary ya kira yi magoya bayansa da su dakatar da dukkanin harkoki domin a tsayar da kasar wuri a matsayin ci gab da nuna kin amincewa da sakamamon zabe.

A can garin Marwa dake a matsayin babban birnin Arewacain kasar,dukkanin harkokin yau da kullum sun tsaya kacokau.

Wani dan kasuwa ya bayyana cewa, rufe kasuwa a wurinsu abu ne mai wahala,amma za su yi ne saboda tsoron kar a kona musu shaguna.

Haka nan kuma ya ce, kasuwar ma ta tsaya cak saboda babu masu saye da suke zuwa.

Da akwai garuruwa da dama da su ka zama kango, saboda kaurewa harkokin yau da kullum da mutane su ka yi a ci gaba da nuna kin yarda da sakamanon zabe.

Wani dan kasuwar mai suna Abdulaziz ya ce; Suna jin tsoron abinda zai faru saboda babu jami’an tsaro da za su ba su kariya.

Wani dalibin jami’a mai suna Gringa Dieudonne ya bayyana cewa gabanin rikicin zabe su 50 ne a cikin ajinsu,amma yanzu su 20 ne kadai suke zama saboda an kauracewa garin.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari