Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a zaman lafiya da hakuri a tsakanin al’ummar garin Rimin Zakara sakamakon rikicin filaye da ya barke tsakanin al’umma da Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).

 

Sarkin ya yi wannan roko ne a ziyarar da ya kai yankin bayan dawowarsa daga aikin hajji.

 

Da yake jawabi ga al’ummar yankin, Sarkin ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a rikicin tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka jikkata cikin gaggawa.

 

“Dole ne mu yi wa wadanda suka rasu addu’a da kuma baiwa iyalansu ikon jure wannan rashi, Allah ya sa wannan ya zama na karshe a cikin irin wannan mummunan lamari a cikin al’ummarmu,” inji shi.

 

Sarkin ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu kamun kai tare da ba da damar bin doka da oda, yana mai jaddada cewa tashin hankali yana haifar da karin wahala ne kawai.

 

“Lokacin da tashin hankali ya barke mutanenmu ne ke shan wahala, babu wani barna ko zubar da jini da zai magance matsalar, dole ne mu hada kai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma,” in ji shi.

 

Da yake la’akari da sarkakiyar rigimar da aka kwashe shekaru ana yi, Sarkin ya bayyana cewa al’umma da jami’a suna da’awar mallakar fili a bisa doka. Ya jaddada bukatar a samar da shawarwari ta hanyar kotu da kuma tattaunawa tare da hukumomin da abin ya shafa.

 

“Bai kamata wannan al’amari ya kasance mai sarkakiya ba, idan har shari’ar ta kasance a gaban kotu, dole ne a warware ta da kwararan hujjoji, dole ne mu zauna da dukkan bangarorin da abin ya shafa domin samun maslaha mai dorewa,” inji shi.

 

Domin samar da zaman lafiya, Sarkin ya bayyana shirin kafa wani kwamiti da zai kunshi wakilai daga dukkan masu ruwa da tsaki, da suka hada da gwamnatin jihar, da hukumomin BUK, da hukumomin tsaro, da shugabannin al’umma, domin magance matsalar.

 

“Za mu hada hannu da Gwamna, da hukumomin BUK, da jami’an tsaro don tabbatar da an yi adalci, amma idan kun sayar da filayen ku, kun karbi diyya, to ku amince da gaskiyar lamarin,” in ji shi.

 

Sarkin ya kammala ziyarar tasa inda ya bukaci mazauna yankin da su baiwa zaman lafiya da hadin kai fifiko, yana mai jaddada cewa babu wata kasa ko dukiya da ta kai asarar rayukan bil’adama.

 

“Rayuwar mutum daya ta fi duk duniya daraja, dole ne mu hada kai don ganin ba a sake samun irin wannan bala’i ba, adalci zai yi nasara, kuma Allah yana tare da masu tsayawa kan gaskiya.”

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sarki

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban

Sojojin mamayar Isra’ila 5 ne suka halaka yayin da wasu 10 suka jikkata a wani gagarumin farmaki da aka kai musu a arewacin Gaza

Sojojin mamayar Isra’ila 5 ne suka sheka lahira sannan wasu akalla 10 suka jikkata a wani gagarumin farmaki da ‘yan gwagwarmaya suka kai a Beit Hanoun da ke arewacin zirin Gaza. Har yanzu wani sojan Isra’ila ya bace kamar yadda kafafen yada labaran haramtacciyar kasar Isra’ila suka ruwaito.

Cibiyar yada labaran Falasdinu ta watsa rahoton cewa, lamarin ya faru ne a lokacin da s’yan gwagwarmaya suka tayar da bam a cikin wata motar sojin Isra’ila mai sulke dauke da sojoji, sannan suka nufi wani mutum-mutumi da ke dauke da harsashi da makami mai linzami a lokacin da ake shirya shi.

Hare-haren dai sun auka ne kan dakarun ceto na Isra’ila da suka garzaya zuwa wurin, yayin da mazauna birnin Ashkelon suka ji karar fashewar wani babban bam, a cewar shafukan yanar gizo na Isra’ila, inda suka ce daya daga cikin wadanda suka jikkata wani babban jami’i ne.

Sojojin da aka kai wa harin na sashen injiniyan Yahalom ne, wanda ke da alhakin yin tarko da kuma tayar da bama-bamai a gidajen Falasdinawa a zirin Gaza, a cewar wakilin Al Jazeera na Falasdinu, Najwan Samri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban
  • Kakakin Rundunar Izzuddeen Qassam ya Bayyana Yadda Suka Yi Kofar Rago Ga Sojojin Mamayar Isra’ila
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi
  • China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS
  • Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza