Sarki Sanusi ya ziyarci Rimin Zakara, ya yi kira da a kwantar da hankula kan rikicin filaye
Published: 6th, February 2025 GMT
Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a zaman lafiya da hakuri a tsakanin al’ummar garin Rimin Zakara sakamakon rikicin filaye da ya barke tsakanin al’umma da Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).
Sarkin ya yi wannan roko ne a ziyarar da ya kai yankin bayan dawowarsa daga aikin hajji.
Da yake jawabi ga al’ummar yankin, Sarkin ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a rikicin tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka jikkata cikin gaggawa.
“Dole ne mu yi wa wadanda suka rasu addu’a da kuma baiwa iyalansu ikon jure wannan rashi, Allah ya sa wannan ya zama na karshe a cikin irin wannan mummunan lamari a cikin al’ummarmu,” inji shi.
Sarkin ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu kamun kai tare da ba da damar bin doka da oda, yana mai jaddada cewa tashin hankali yana haifar da karin wahala ne kawai.
“Lokacin da tashin hankali ya barke mutanenmu ne ke shan wahala, babu wani barna ko zubar da jini da zai magance matsalar, dole ne mu hada kai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma,” in ji shi.
Da yake la’akari da sarkakiyar rigimar da aka kwashe shekaru ana yi, Sarkin ya bayyana cewa al’umma da jami’a suna da’awar mallakar fili a bisa doka. Ya jaddada bukatar a samar da shawarwari ta hanyar kotu da kuma tattaunawa tare da hukumomin da abin ya shafa.
“Bai kamata wannan al’amari ya kasance mai sarkakiya ba, idan har shari’ar ta kasance a gaban kotu, dole ne a warware ta da kwararan hujjoji, dole ne mu zauna da dukkan bangarorin da abin ya shafa domin samun maslaha mai dorewa,” inji shi.
Domin samar da zaman lafiya, Sarkin ya bayyana shirin kafa wani kwamiti da zai kunshi wakilai daga dukkan masu ruwa da tsaki, da suka hada da gwamnatin jihar, da hukumomin BUK, da hukumomin tsaro, da shugabannin al’umma, domin magance matsalar.
“Za mu hada hannu da Gwamna, da hukumomin BUK, da jami’an tsaro don tabbatar da an yi adalci, amma idan kun sayar da filayen ku, kun karbi diyya, to ku amince da gaskiyar lamarin,” in ji shi.
Sarkin ya kammala ziyarar tasa inda ya bukaci mazauna yankin da su baiwa zaman lafiya da hadin kai fifiko, yana mai jaddada cewa babu wata kasa ko dukiya da ta kai asarar rayukan bil’adama.
“Rayuwar mutum daya ta fi duk duniya daraja, dole ne mu hada kai don ganin ba a sake samun irin wannan bala’i ba, adalci zai yi nasara, kuma Allah yana tare da masu tsayawa kan gaskiya.”
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarki
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp